Shaye-Shaye A Garin Gusau (5)

    Kundin Binciken Neman Digirin Farko (B.A Hausa) Wanda Aka Gabatar A Sashen Harsuna Da Al’adu Jami’ar Tarayya Gusau.

    Shaye-Shaye A Garin Gusau (5)

    NA

    BASHAR ISYAKA

     

    Magani

    BABI NA HUÆŠU

    4.0 GABATARWA

    Wannan babi zai tattauna ne a kan hanyoyin kawadda shaye-shaye wuÉ—anda sunka haÉ—a da: Shigowar kungiyoyin addinai, Æ™oÆ™arin al’umma ga kawadda shaye-shaye, Æ™oÆ™arin kungiyoyin da ba na gwamnati ba, Æ™oÆ™arin da hukuma ke yi ga kawar da É—abi’ar shaye-shaye a cikin al’umma, da sauransu.

     

    4.1 SHIGOWAR ƘUNGIYOYIN ADDINAI

    Addinai da dama sun yi hani a kan wannan É—abi’ar ta shaye-shaye musamman ma addinin musulunci Allah (SWA) ya faÉ—a a cikin littafinsa mai girma “Ya ku masu imani ka da ku sha giya ko wani abu da ke sa maye…..” Sannan Manzon Allah (SAW) ya ce, “duk wanda ya sha giya sau ashirin Allah ba ya tare da shi”. Bayan haka, Annabi (SAW) ya ce, Allah ya la’anci mai shan giya da mai sayar da ita da mai aikinta da mai É—aukar ta da wanda ya taimaka wajen daukar ta, da kuma wanda ya ci kuÉ—inta. Kuma Allah (SWA) ya ce; “Mutane uku ba su shiga al-jannah, daga cikinsu akwai mashayin giya”, bugu da Æ™ari Annabi (SAW) ya ce; “Wanda ya sha giya kamar mai bautar gunki ne”. Wannan shi ne hanin da addinin musulunci ya yi dangane da É—abi’ar shaye-shayen abubuwa masu sa maye.

     

    Haka kuma, addinin kiristanci shi ma ya yi hani a kan wannan mummunar É—abi’ar, domin kuwa a cikin littafin Injila (Bible) wanda aka saukar ma Annabi Isah (AS), Allah ya ce “Na haramta maku cin mushe, da jini, da alade, da zina da sihiri da giba da duk abinda ke sa maye…..” (Bible babi na É—aya aya ta goma).

     

    Bayan addinin kiristanci, haka ma sauran addinai da dama su ma sun yi hani a kan  wannan shaye-shaye kamar yadda addinin musulunci da na kiristanci suka yi hani. Sun yi hani da wanda yake cikin halin maye ya yi wakilci ko jagoranci a cikin al’amuran yau da kullum. Haka kuma bayan hani da addinin musulunci da na kiristanci suka yi, shaye-shaye yana karya tattalin arzikin Æ™asa sannan kuma yana illa ga lafiyar mai yin sa.

     

    4.2 ƘOƘARIN AL’UMMA GA KAWAR DA SHAYE-SHAYE

    Shaye-shaye É—abi’a ce mai zubar da mutuncin mutum. Akasari mutane kan É—auki wanda ke shaye-shaye a matsayin mutumin banza, kuma marar mutunci. A taÆ™aice dai duk mai wannan É—abi’ar ta shaye-shaye komi kuÉ—insa ko iliminsa mutuncinsa da Æ™imarsa kan zube a idon jama’a idan yana shaye-shaye.

     

    Mutane kan kalli mutumin da ke shaye-shaye kamar dabba, domin dabba ita ce ba ta san abin da zai hallaka taba, sai in ta ji ya cimma ta. To haka nan mutumin da ke shaye-shaye yake. Saboda su waÉ—annan kaya na barasa da yake sha suna haifar masa da cututtuka daban-daban a cikin jikinsa. Amma saboda dabbanci (rashin kaifin hankali), ba zai gane abin da ke halaka shi ba.

     

    Haka kuma wasu jama’a kan É—auki masu wannan É—abi’a tamkar mahaukata, domin idan mashayi yana cikin halin maye za ka ga wani lokaci har bugu yake yi. Kuma sukan yi abubuwa kamar mahaukata, saboda duk wani abu da mahaukaci ke yi shi ma a wannan lokaci zai iya yin sa, domin ba ya a cikin hankalinsa. Wannan ne ya sa mutane ba su É—auki wanda ke shaye-shaye a matsayin cikakken mutum ba. Kuma za ka ga mutane suna kyamar shi da ya wakilcesu a al’amurran yau da kullum domin suna ganin ba ya da cikakken hankali.

     

    A taÆ™aice dai al’umma kan É—auki duk mutumin da ke shaye-shaye a matsayin mutumin banza.

     

    4.3 ƘOƘARIN ƘUNGIYOYIN DA BA NA GWAMNATI BA

    Kasancewar shaye-shaye mummunar É—abi’a ce da ke zubar da mutuncin É—an Adam da kimarsa, akwai Æ™ungiyoyi masu zaman kansu waÉ—anda suka tashi tukuru wajen yaÆ™i da wannan mummunar É—abi’a ta kwankwaÉ—ar barasa. WaÉ—annan Æ™ungiyoyin sun haÉ—a da Hukumar Hizba da ‘yan banga da ‘yan agaji da sauran Æ™unyoyi na cikin unguwani. HaÆ™iÆ™a waÉ—annan Æ™ungiyoyi ba Æ™aramar rawa suke takawa ba wajen magance wannan É—abi’a. Sannan kungiyoyin malamai tun daga na gwamnatin tarayya har na jihohi musamman ma Malaman addini na cikin wannan jiha suna Æ™oÆ™ari Æ™warai wajen yin wa’azi tare da faÉ—akar da masu shaye-shaye, game da illolin da shaye-shaye ke haifarwa a al’adance da kuma a addinance.

     

    Sannan kuma Æ™ungiyoyi irin su Æ™ungiyar ‘yan jarida watau (Ratawo) gidajen rediyo da talabijin da Æ™asidu da mujallu suna taimakawa matuÆ™a wajen faÉ—akarwa ga illolin da ke tattare a cikin wannan mummunar É—abi’a ta shaye-shaye.

     

    HaÆ™iÆ™a wannan faÉ—akarwar da suke yi dare da rana tana taimakawa ainun wajen kawar da wannan mummunar É—abi’ar ta shaye-shaye.

     

    Bayan wannan akwai wata Æ™ungiya mai zaman kanta, ita wannan Æ™ungiya ta matasa ce wadda ke sa ido Æ™warai da gaske domin ganin an kawar da wannan É—abi’ar ta shaye-shaye a cikin wannan gari na Gusau.

     


     

    4.4 ƘOƘARIN DA HUKUMOMI KE YI GA KAWADDA ÆŠABI’AR SHAYE-SHAYE A CIKIN AL’UMMA

    A Æ™oÆ™arin da hukumomi ke yi na ganin cewa ta kawar da wannan mummunar É—abi’ar ta shaye-shaye, ta kafa Æ™ungiyoyi da dama. Irin waÉ—annan Æ™ungiyoyin sun haÉ—a da Æ™ungiyar yaÆ™i da shan miyagun Æ™wayoyi (NDLEA). Ita wannan Æ™ungiya ta taimaka ainun wajen binciko masu shaye – shaye da kuma hukunta su.

     

    A cikin shekarar (1983) shan miyagun Æ™wayoyi a Najeriya ya zama ruwan dare. Saboda haka ne gwamnatin tarayya ta mulkin soji Æ™arÆ™ashin jagorancin janar Muhammad Buhari a cikin shekara ta (1984) ta yi Æ™oÆ™arin magance wannan mummunar É—abi’ar, inda ta Æ™irÆ™iro wani shiri na musamman watau (laifukkan gobe). Shi wannan shiri an shirya shi ne domin faÉ—akar da masu wannan É—abi’a. Sannan gwamnati ta samar da dokoki domin hukunta masu wannan É—abi’a ta shaya-shaye.

     

    Haka zalika, da aka samu canjin gwamnati a shekara 1985 a ƙarƙashin jagorancin janar Ibrahim Badamasi Babangida, Gwamnatinsa ta ba da ƙarfi ne wajen hana shan ƙwayoyi da barasa da kuma hana yawace yawacen banza a cikin ƙasa. Wannan gwamnati ta ɗauki alkawarin bincikowa da kuma hana amfani da kayan barasa a cikin Najeriya.

     

    Sannan kuma a shekarar 2000 ma gwamnatin jihar Zamfara a Æ™arÆ™ashin jagorancin Alhaji Ahmad Sani Yariman Bakura ta É—auki babban mataki ga dukkan masu wannan É—abi’a ta shaye-shaye. Ta hanyar rufe duk wani wuri da ake shaye-shaye a cikinsa. Haka kuma da É—aukar matakin hukunta duk wanda aka kama yana shan wani abu mai sa maye bayyane ko a É“oye. Sanadiyar haka gwamnatin jihar Zamfara ta É—auki aniyar magance matsalolin kwankwaÉ—ar barasa musamman ma a cikin Æ™aramar hukumar mulki ta Gusau. Wannan gwamnati ta lashi takobin ganin cewa Æ™wanÆ™waÉ—ar miyagun Æ™wayoyi zai zama tarihi a wannan jiha.

     

    Bisa nazari da Æ™iyastawa daga shekara ta (2000-2007) an samu sauÆ™i yadda ya kamata na kawar da É—abi’ar shaye-shaye a cikin garin Gusau.

     

    4.5 KAMMALAWA

    Wannan babi na huÉ—u yana bayani ne a kan hanyoyin kawadda shaye-shaye waÉ—anda suka haÉ—a da shigowar Æ™ungiyoyin addini da Æ™oÆ™arin al’umma ga kawar da shaye-shaye. Haka kuma da Æ™oÆ™arin kungiyoyi da ba na gwamnati ba suke yi, da hukumar hana sha da fataucin miyagun Æ™wayoyi ke yi ga kawar da É—abi’ar shaye-shaye a cikin al’umma.

    No comments:

    Post a Comment

    ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.

    HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.