Kisan Gillar Hanifa

    Fasihi Abdullahi Abubakar Lamido ne ya shirya wannan waƙa domin jajanta kisan gilla da aka yi wa Hanifa.

    Hanifa

    Da sunan Jalla Sarkinmu

    Salati gun Habibinmu

    Iyalai har sahabbanmu 

    Ina baiti cikin hammu

    Ba zan iya tsai da kwalla ba 


    Idan kun lura yau hakkun 

    Hakika mun shiga ukku

    Muna tafiya cikin tasku 

    Ku lura da duk makwabtanku

    Ashe jiya ba kamar yau ba 


    Muna karshe na zamani

    Mutane babu addini 

    A zuciya babu imani

    Rashin kunya a yau launi 

    Kamar ba a san da Allah ba 


    A dauki mutum a sace shi 

    A firgita duk iyayenshi

    A je a ci mar mutuncinshi

    A karbi kudi ga danginshi 

    Ba za a ji tausayi nai ba 


    Ku dubi Hanifa yarinya 

    Iyaye sun mata tarbiyya 

    Ta boko har Islamiya 

    Suna fatar ta dau hanya

    Ashe burin ba zai cika ba


    Kwatsam burinsu ya yanke 

    Da jin dadinsu an dauke 

    Da koyarwa mutum ya fake 

    Ashe mugun hali ya rike 

    Da dai ba malami ne ba


    Haba Abdulmalik Tanko 

    Bugaggen mallamin boko 

    Iyaye sunka baka riko

    Ka  bata guba cikin koko

    Ka daddatsa ta kamar dabba 


    Saboda bakin rashin kunya 

    La'ini mai bakar aniya

    Ya je ya tsaya a kan hanya 

    Ya dauki Hanifa yarinya 

    Ashe zai je ya bata guba 


    Ganin Uncle tana murna 

    Zuma a gareta ka nuna 

    Ashe tarko baki ka dana 

    Zatonta karimci zai nuna 

    Ashe bai shirya kirki ba 


    Ka karta ka datsa gawanta 

    Da kanka ka tona raminta 

    Ka je ka ka bunne gawarta 

    Ka karbi kudin iyayenta 

    Da dai ba ka tausaya musu ba 


    Ina ka baro tunaninka

    Da imani da rahamarka 

    Ka kama mutum da hannunka 

    Ka karshi ka daddatse da wuka 

    Ba za ka tuna da Allah ba


    Abun haushin da matarka 

    Ta aure har da 'ya'yanka 

    Ka mance batun mutuncinka 

    Ka dau hanya ta 'yan iska 

    Da dai ba ka yo tunani ba 


    Ka gan ka ya salihin bawa 

    Ashe keta kaka shiryawa 

    Kudin banza kake yunwa 

    Kawai ka zabi tabewa 

    Da dai baka zabi tsira ba 


    Hukunci dole zai hau ka

    Fa tabbas za ka sha duka 

    Kisa ita ce makomarka

    Saboda bakin hali naka 

    Wallahi ba za mu yafe ba 


    Sanan ka bata sunanka 

    Da ma sunan iyalanka 

    Da tozarci ma 'ya'yanka

    Irinka halinka ba shakka 

    Yana jawo tsiya babba 


    Idan ba a tsire wannan ba

    Idan ba a mai hukunci ba 

    Idan ba a ba shi horo ba 

    Kasar ga ba za mu huta ba 

    Bala'i ba za shi kare ba 


    A kan lamarinta nai kwalla 

    Ina maimaita la haula

    Irin wannan kisan gilla 

    Yana janyo fushin Allah 

    Mai yinsa ba zai yi karko ba


    Abin ya bani mamaki

    A zuci har ya min miki 

    Ina tafiya ya min birki 

    Gaba daya ya hanan aiki 

    Ba zan iya manta wannan ba 


    Cikin lamarin da daurin kai

    Halin wannan akwai cin rai 

    Mutane sun zamo birrai 

    Gaba daya ba batun tausai 

    Kamar ma ba Musulmi ba 


    Ilahi na yi rokonka 

    Ka kai rahama ga baiwarka

    Hanifatu don buwayarka 

    Iyaye nata ko dukka 

    Hada su da dangana Rabba 


    Ka sa nitsuwa a zucinsu

    Ilahu ka kwaci hakkinsu 

    Ka daukaka martabobinsu 

    Maye musu wanga 'ya tasu 

    Tsare su da mai halin dabba


    A yau jama'a mu hankalta 

    Mu tashi mazammu har mata 

    Mu taimaki duk iyayenta 

    Mu je mu tsaya wa hakkinta 

    Mu kauce wa fushin Rabba 


    Ina 'yan tutiyar 'yanci 

    Ku taso babu lalaci

    Ku bar zance na turanci

    Ku kama fada da zalunci

    Ku bar zance na kankamba 


    Ta can ko na hangi wani lauya 

    Ba Fir'aune maras kunya 

    Ya na so zai yi jayayya 

    Ya kare baki maras kunya 

    Ya ce wai bai yi laifi ba 


    Iyaye hattara tilas

    Ku lura da masu yin cikas 

    Barayi su da "kidnappers"

    Gama a kasarmu ba tabbas 

    Ba za mu aminci kowa ba 


    Mutane sun ki bin Allah 

    Kawai sai dai bidar "dollar"

    Ta hanyar yin kisan gilla 

    Abin ya kai ga La haula 

    Ba zan iya fayyacewa ba 

     

    A nan zan kare maqqala 

    Amir Lamido Abdallah 

    Ina roko wajen Jalla 

    Ka yafe min dukan zalla

    Ilahal Arshi na tuba 


    19 Jumada Al-Akhirah 1443

    No comments:

    Post a Comment

    ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.

    HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.