Hukuncin Haɗa Sittu Shawwal Da Ramuwar Ramadan

    𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

    Assalamu alaikum Malam idan ana binka ramuwar azumi za ka iya niyya biyu: wato da nufin sittu shawwal da ramuwar Ramadana a guda ɗaya? don Allah mlm taimaka min da bayani.

    𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

    Wa'alaikum assalamu, To 'yar'uwa kowanne daban ake yin sa, saboda manufarsu ta banbanta, don haka ba za a haɗa su da niyya ɗaya ba, kamar yadda ake yi a wankan janaba da wankan juma'a, za mu fahimci haka, a cikin faɗin Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi: "Duk wanda ya azumci Ramadana sannan ya biyar da kwanaki shida na Shawwal, Allah zai ba shi ladan wanda ya yi azumin shekara" Muslim ya rawaito shi a hadisi mai lamba ta: 1164, kin ga wannan yana nuna Ramadan daban, sittu-shawwal daban.

    Fadin Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi: "Sannan ya biyar da kwanaki shida na Shawwal" ya sa wasu malaman sun tafi a kan cewa: bai halatta ayi sittu-shawwal ba, sai bayan an kammala ramuwar Ramadan. Kamar yadda ya zo a: sharhurmumti'i 6\443.

    Allah ne ma fi sani.

    Amsawa:-Dr. Jamilu Zarewa.

    Ga Masu Buƙatar Shiga Wannan Group Zaku iya bi ta Links ɗin mu...

    𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

    https://chat.whatsapp.com/BXjuXb1WxX99NV3OsXPnLV

    𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

    Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

    𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

    https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi


    No comments:

    Post a Comment

    ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.

    HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.