Hukuncin Mijin Da Ya Rubuta Wa Matarsa Saki, Sai Ya Fasa Ba Ta Takardar

    𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

    Mutum ne yake so ya saki Matarsa, har ma ya rubuta takarda dauke da saki uku a ciki, amma dagaba ya sai ya fasa ba ta takardar, Shin yanzu ta saku kenan ko ba ta saku ba??

    𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

    Abin da Ma'abota Ilimi sukace dangane da wannan Mas'ala shi ne: idan Miji ya rubutawa Matarsa takardar saki, to hukunci yana komawa ne zuwa ga niyyar sa a lokacin da yake yin rubutun, idan dama a lokacin ya yi haka ne da niyyar saki to ko shakka babu cewa Matarsa ta saku ko ya ba ta takardar ko bai ba ta ba, amma idan a lokacin da yake rubutun ba niyyarsa ya saketa ba, sai dai ya yi ne kawai saboda da nufin idan nan gaba zai sake ta basai ya sake rubutawa ba, ko kuma ya rubuta ne da nufin ya baƙanta mata rai ko dan ya tsoratar da ita saboda ta dena aikata wani abu da take yi maras kyau, amma bawai ya yi ne da kudurin nufin ya saketa ba, dadai wasu abubuwa makamancin hakan, Malamai suka ce a irin wannan yana yi Matarsa tana nan ba ta saku ba, domin Manzon Allah(ﷺ) Ya ce:

    "إنما الأعمال بالنيات......"

    MA'ANA:

    Haƙiƙa Dukkan ayyuka (na ibada) ana yinsu ne da niyya..........

    Kuma wannan ita ce fatawar waɗannan Malamai kamar haka: -Imamu Malik -Imamu Abu-Hanifa -Imamush-Sha'abiy -Imamun-Nakh'iy -Imamuz-Zuhriy -Imamush-Shafi'iy. Da Sauran Mafi yawa daga cikin Ma'abota Ilimi, sukace shi dai rubutu hukuncinsa kamar kinaya ce, ita kuma kinaya ba a tabbatar da saki da ita sai in da niyya, abisa ga zancen da yafi inganci, amma inda zai fito fili ƙarara ya furta da bakinsa ya ce na sakeki to ko shakka babu anan Matarsa tasaku.

    Danhaka kenan idan Miji ya rubutawa Matarsa takardar saki mai ɗauke da lafazin da ya ɗauki Ma'anar saki a fili, kuma ya rubuta hakan da niyyar ya saketa ɗin shikenan Matarsa ta saku, amma idan saki biyu ne ya rubuta ko kuma saki uku magana mafi inganci za a ɗauke shi ne amatsayin saki ɗaya kawai, duk da cewa Mazhabin MALIKIYYA sun tafi ne a kan cewa idan mutum ya saki mace saki uku a lokaci ɗaya to kawai ta saku, amma magana mafi inganci za a ɗauke shi ne amatsayin saki ɗaya kamar yadda Malamai da yawa suka yi bayani a kan haka.

    шαʟʟαнυ-тα'αʟα α'αʟαмυ

     Mυѕтαρнα Uѕмαи

     08032531505

    Ga Masu Buƙatar Shiga Wannan Group Zaku iya bi ta Links ɗin mu...

    𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

    https://chat.whatsapp.com/BXjuXb1WxX99NV3OsXPnLV

    𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

    Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

    𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

    https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi

    ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

    **************************

    Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

    Questions and Answers

    No comments:

    Post a Comment

    ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.

    HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.