Bambancin Ɗan Musulmi Da Ɗan Kafiri

    𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

    Assalamu Alaikum, Malam dan Allah ya bambancin diyar musulmi da na kafuri?

    𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

    Wa'alaikumus Salam, Malamai sun yi saɓani game da matsayin ‘ya’yan waɗanda ba musulmi ba ta fuskar matsayinsu a duniya da kuma matsayin su a lahira.

    Daga cikin abin da malamai suka ce shi ne: matsayin ɗa yana bin iyayensa ne, idan kafirai suka haifi yaro, to wannan yaron yana bin su ne a hukuncin al'amuran duniya, wato ko mutuwa ya yi ba za a yi masa sallah ba, kuma ba za a birne shi a maƙabartar Musulmai ba, Amma matsayinsu a lahira wasu malaman sun ce za a yi masu jarabawa ce, idan suka yi wa Allah biyayya a kan wannan jarabawar sai a sa su a Aljannah, idan kuma ba su yi biyayya ba sai a kai su akasin Aljannah, wato kamar hukuncin waɗanda saƙon Manzanci bai zo masu ba kenan (Ahlul Fatra).

    Wato dai matsayinsu a duniya ana riskar da shi ne da matsayin iyayensu, amma a haƙiƙanin lamarin su ba kafirai ba ne, lallurar raino ce ta sa su a ƙarƙashin kafirai, saboda yaro ba zai iya rayuwa ba tare da mai raino ba.

    Akwai kuma malaman da suke ganin idan ‘ya’yan kafirai suka mutu kafin balaga, to Aljannah za a sa su, hujjarsu ita ce tun da Annabi ﷺ ya ce: "Duk wani abin haihuwa ana haifansa ne a kan Musulunci, sai iyayensa su mayar da shi Bayahude, ko Banasare, ko Bamajushe".

    Bukhariy (1385), Muslim (2658).

    Don ƙarin bayani a kan wannan sai a duba Ahkámu Ahliz Zhimma, na Ibnul Ƙayyim.

    Su ko ‘ya’yan Musulmai ai duk matsayinsu da hukuncinsu irin na musulmai ne a duniya da lahira.

    Allah ne mafi sani.

    Jamilu Ibrahim Sarki, Zaria.

    Ga Masu Buƙatar Shiga Wannan Group Zaku iya bi ta Links ɗin mu...

    𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

    https://chat.whatsapp.com/FmJ5Ojsns1KFolTP8ƙu9GT

    𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

    Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

    𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

    https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi

    ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

    **************************

    Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

    Question and Answers in Islam

    No comments:

    Post a Comment

    ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.

    HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.