Haddi A Musulunci 01

    Haddi A Musulunci 01

    Haddi kankarar zunubi ne ga wanda aka tsayarwa tun anan duniya.

     Daga Ubadatu Ɗan Samitin (R.A) Ya ce:

    Mun kasance a tare da Manzon ALLAH {s.a.w} a wani majalasi sai ya ce:

    Zakuyimin alƙawari akan baza kuyi shirka da ALLAH ba, baza kuyi zina ba, ba za kuyi sata ba, kuma ba zaku kashe ran da ALLAH ya haramta kashewa ba, face sai da gaskiya,

     Wanda ya cika wannan alƙawarin daga cikinku, to ladansa yana wajen ALLAH,

     Wanda kuwa ya aikata wani abu daga cikin waɗannan abubuwa sai akayi masa haddi (hukunci ) a duniya, to wannan shi kankarar zunubi ne a gareshi.

     Wanda kuwa ya aikata ɗaya daga cikinsu, sai ALLAH ya rufa masa asiri, to lamarinsa yana ga ALLAH, idan yaso ya yi masa rahma, idan yaso ya yi masa azaba.

    Sannan a wani hadisin kuma Manzon ALLAH {s.a.w} ya ce: Tsayar da haddi a bayan ƙasa shi yafi alkhairi ga mazaunan cikinta daga ruwan saman kwana arba'in.

    [Nisa'i ne ya rawaito shi.

    Waɗannan hadisai suna magana ne akan hukunci da littafin ALLAH akan wanda ya aikata ɗaya daga cikin laifukan da aka lissafo a cikin hadisin dama waɗanda ba a lissafo ba.

     Idan mutum ya aikata zina mai aure ne ko mara aure, matar aure ce ko buduruwa, saurayinne ko mai aure, sai aka kama mutum, kuma aka sami shaidu guda huɗu (4) sai alƙali ya tambayesu ɗaya bayan ɗaya, kuma ko wanne daban, suka tabbatar da sun gansu turmi da taɓarya, kuma bakinsu ya zo ɗaya, to sai ayiwa wanda aka kama ɗin hukunci.

     Wannan hukuncin da aka yiwa mutum na zina ne, ko na sata ko zinar mai aure ko na kisa, to ana yiwa mutum shikenan, nan take ALLAH zai kankare masa zunubansa.

     Idan kuwa mutum ya aikata laifin zina ko kisa ko waninsa sai ALLAH ya rufa masa asiri, babu wanda ya ganshi, to kada ya tonawa kansa asiri, sannan kuma Annabi {s.a.w} yace sakamakonsa yana ga ALLAH idan yaso ya yafe masa, idan yaso kuma ya yi masa azaba.

     Idan kuma mutum ya gaggauta tuba tun anan duniya, to ALLAH mai jine mai ganine, mutuƙar ka yi tuba mai kyau, ALLAH zai gafarta maka abinda ka aikata na zunubanka baki ɗaya da wanda ka sani da wanda baka sani ba.

     Babu laifin da ALLAH baya yafewa mutuƙar an nemi yafiyarsa, sai haƙƙin wani, haƙƙin waninma akwai irin wanda ALLAH yake yafewa, mutuƙar babu son zuciya da ganganci a cikinsa.

    ALLAH ka bamu ikon aiki da abinda muka karanta.

    ALLAH ka gafarta mana zunubanmu baki ɗayanmu.

    Duk mai neman ƙarin bayani ya yi mana magana ta private.

    ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

    **************************

    Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

    Question and Answers in Islam

    No comments:

    Post a Comment

    ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.

    HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.