Hukuncin Auren Matar Da Aka Ɗauki Tsawon Lokaci Ba'asan Inda Mijinta Yake Ba:

    𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

    Mace ce akanemi Mijinta aka rasa, bayan ta yi idda har ta auri wani mijin kwatsam kuma sai ga Mijinta na farko ya dawo, to yanzu a cikin mazan guda biyu ita Matar waye a cikinsu??

    𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

    Dangane da wannan Mas'ala ta hukuncin auren Matar da akaɗauki tsawon lokaci ba'asan inda Mijinta yakeba, wataƙila harma anhaƙura anfidda rai dashi har ta auri wani Mijin, to kuma kwatsam bayan ta yi aure saiga tsohon Mijinta ya dawo, to wai yanzu Matar ta waye a cikin su biyun? Alal-Haƙiƙa Malamai Ahlul-Ilmi sun yi maganganu daban-dabam akan wannan Mas'ala:

    1. Ƙauli nafarko shi ne, mafi yawan Malaman dake Mazhabobin SHAFI'IYYA, HANAFIYYA, HANABILA, suntafine akan cewa shi wannan tsohon Mijinnata na farko da ya dawo shi ne Mijinta domin Asali dama Matarsace, danhaka auren da'aka ɗaura mata da wancan Mijin nabiyu, to ayanzu sunansa Ɓataccen Aure domin ba a buƙatar wai sai yace yasaketa, amma idan Mijin nabiyu yasadu da'ita to shikenan taci Sadaƙinta, idankuma sunhaifi 'Ya'ya tare dashi to za a jingina masa 'Ya'yansane zuwa gareshi amatsayin 'Ya'ya na Halal, za suci gadonsa shima zai'iyacin gadonsu, saboda kasancewar (Shubuha) r da ta faru atsakani, Saidai kawai yanzu ita Matar zata zaunane ta yi iddar wancan Mijin nabiyu, daga nan sai suci gaba da zama tare da asalin Mijinta ba tare da ansake wani ɗaurin aureba, Saidai Mazhabin HANAFIYYA sunkafawa Matar Sharaɗin cewa baza ta yi aureba har sai intasamu labarin tabbacin cewa Mijinnata yamutu kokuma ya aikomata cewa yasaketa, daga cikin Hujjojin Malaman dake kan wannan fahimta sunkafa Hujja da abin da aka ruwaito daga dukkan waɗannan Sahabbai:

    (1)-Usman-Ɗan-Affan

    (2)-Umar-Ɗan-Kaɗɗab,

    (3)-Aliyu-Ɗan-Abi-Ɗalib,

    (4)-Abdullahi-Ɗan-Abbas,

    (5)-Abdullahi-Ɗan-Zubair

    Cewa dukkansu sun yi hukunci ne akan cewa Mijin farko shi ne Mijinta, kuma ba'asamu wani Sahabi ko guda ɗaya da ya saɓamusu akan hakanba, Aʟʟαн(ﷻ) Yaƙara yarda agaresu baki ɗaya,

    2. Ƙauli nabiyu kuma shi ne, Mazhabin MALIKIYYA suntafine akan cewa idan Mijinta nafarko ya dawo bayan Matar tagama iddarsa hartayi aure kuma Mijin yasadu da'ita, to ayanzu kam bashida iko a kanta tunda ta yi aure danhaka sukace Mutumin da ta aura nabiyun shi ne Mijinta, amma sukace idan baikai ga saduwa da'itaba to Mijita nafarko shi ne yafi cancanta da'ita.

    Saidai magana mafi inganci anan ita ce, wannan Matar tana ƙarƙashin igiyar auren Mijintane nafarko da ya dawo, wannan kenan, to amma idan ya dawo yatarar har anriga anrabe dukiyarsa amatsayin gado to yanzu ya za'ayi kenan? Dukkan Mazhabobin nan guda huɗu sun yi ITTIFAƘINE akance za a dawomasa da dukiyar sane, to amma idan ya kasance dukiyar ta salwantafa ya zama babu ita tuni anriga ankasheta? Anan Sai Malamai suka yi Saɓani, mafi yawan Malamai sukace sai an rama masa anbiyashi dukiyarsa, amma Mazhabin HANAFIYYA sukace babu wata ramuwa da za'ayimasa, kawai abin da ya zo yasamu yakarɓa amma wanda yasalwanta kuma shikenan, Saidai magana mafi inganci idan wanda yaɓata kuma ya dawo gida to za'adawo masa da dukiyarsane dakuma Matarsa.

     وَالـلَّـهُ سُـبْـحَـانَـهُ=وَتـَعَــالـَيٰ أَعْـلَـمُ

    ωαηαη sнιηε gωαяgωαdoη ɗαη αвιηdα ιℓιмιη мυ dαкυмα вιηcιкεηмυ үαкαι zυωα gαяεsнι, dαηнαкα ιdαη αηgα ωαηι кυsкυяε αcιкιη αвιηdα мυкα яυвυтα тo αηα'ιүα ғαɗαкαя dαмυ мυgүαяα, тαяεdα кαωo нυננα мαι ƙαяғι:

    Doмυп пεмαп ƙαяıп вαчαпı sαı αdυвα шαɗαппαп ʟıтαттαғαı καмαя нακα:

     ↓↓↓

    "الموطإ مالك" (2/575)

    "مواهب الجليل" (4/15)

    "بدائع الصنائع" (3/215)

    " كشاف القناع" (5/422)

     AMSAWA

     Mυѕтαρнα Uѕмαи

     08032531505

    Ga Masu Buƙatar Shiga Wannan Group Zaku iya bi ta Links ɗin mu...

    𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

    https://chat.whatsapp.com/JoWs3feDfdyGE9yBsa1RSC

    𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

    Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

    𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

    https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi

    ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

    **************************

    Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

    Question and Answers in Islam

    No comments:

    Post a Comment

    ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.

    HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.