Hukuncin Sakon Gaisuwar Juma'a (Jūma'at-Mubārak)

    𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

    A Shari'ance Mene ne hukuncin Sakon Gaisuwar Juma'a, da'ake ayiwa Mutane ta Text ko Social Media??

    𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

    ​Ko shakka bābu cewa ​Rānar-Jūma'a​ rānāce ta īdi awajen Musulmai, kamar yadda ya zo a Hadīsi cewa ​Mαnzon Aʟʟāн(ﷺ)​ Yāce:​

    ​إن هذا يوم عيد جعله الله للمسلمين، فمن جاء إلي المسجد فليغتسل.......... (رواه إبن ماجه/1098)​

    ​​MA'ANA​​

    ​​Lallai wannan rānāce (Jūma'a) da Aʟʟāн(ﷻ) ya sanyāta amatsayin īdi ga Musulmai, danhaka idan Mutum zaije Masallāci to ya yi wanka,......​​

    ​Dan haka kenan Musulmai sunada ​rānekun īdi​ ne guda uku kawai a Muslunci,​

    ​​-Īdin-Rānar-Jūma'a:​​

    ​​-Īdin-Babbar-Sallāh:​​

    ​​-Īdin-ƙaramar-Sallāh:​​

    ​Saidai ​Īdin-Babbar-Sallāh da Īdin-ƙaramar-Sallāh​ sukan maimaitune aduk Shēkara, amma ​Īdin-Rānar-Jūma'a​ yakan maimaitune duk ​Sāti-Sāti,​​

    ​Amma dangane da abinda yashāfi hukuncin ​Sakonu-Gaisuwar-Jūma'a,​ da Mutāne sukeyi atsakaninsu, kamar irin su:​

    ​​Jūma'at-Karīm,​​

    ​​Jūma'at-Mufīdat,​​

    ​​Jūma'at-Mubārak,​​

    ​​Jūma'at-Ɗayyibat,​​

    ​Dadai sauran makamansu, sai ariƙa aikāwa 'Yan'uwā da abokan arziƙi ta hanyar ​Text-Message,​ kokuma ta ​Social Network,​ Abinda yake a ​Shari'ance​ kamar yadda ​Mālamai​ suka faɗa shi ne, Asali Muslunci yā yardane kawai da ​Gaisuwar Rānekun Īdin-ƙaramar-Sallāh da Babbar-Sallāh,​ sūmā abisa ga wasu lafuzza da ​Shari'a​ ta yarda a yi amfāni dasu, amma gameda ​Gaisuwar-Jūma'a,​ bābu inda ​Shari'a​ ta yi bayānin cewa ayi, danhaka dayawa daga cikin ​Mālamai​ sukace yin ​Gaisuwar-Jūma'a Bid'ace,​ musamman idan yakasance māsu yin hakan suna ƙudurta cewa akwai wani lada da za a sāmu ga duk wanda yayi, to ko Shakka bābu cewa yā zama ​Bid'a,​ domin ba'asamu hukuncin yin hakan a cikin wani ​Nassi​ ko aikin magabāta ba,​

    ​Saidai akwai ​Mālaman​ dasuke ganin cewa idan Mutum ya yi ​Gaisuwar-Jūma'a,​ tare da cewa yāsan bāta da asali a cikin addīni sannan kuma bai ƙudurta cewa yin hakan Sunna bane, kokuma idan Mutum yāyi zai sāmu wani lādā akaiba, kawai suna yine amatsayin ​al'āda​ bawai da sunan addīniba, sukace to bābu wani laifi a kansu dan sunyi, saidai duk dahaka sukace barin yinsa ɗin shīne yafi zamā alkhairi, saboda gudu kada ​Jāhilai su rūɗu​ da cewa hakan ​adiīnine,​ wanda kuma gālibin māsu aika ​Sakon-Gaisuwar-Jūma'a,​ awannan zāmanin zāka sāmu cewa suna yīne danufin sāmun lādā bawai suna yine amatsayin al'ādaba, ​Aʟʟāн(ﷻ)​ dai Ya gānar damu gaskiya kuma yabāmu īkon binta ​Āmīn-Yā-Rabbi,​​

    Doмυп пεмαп ƙαяıп вαчαпı sαı αdυвα шαɗαппαп ʟıтαттαғαı καмαя нακα:​​

     ​​↓↓↓​​

    ​"زاد المعاد" (1/380)​

    ​"الفتاوي الكبري" (2/228)​

    ​​шαʟʟαнυ-тα'αʟα α'α'αʟαмυ

     ​​AMSAWA

     ​Mυѕтαρнα Uѕмαn​

     ​08032531505​

    Ga Masu Buƙatar Shiga Wannan Group Zaku iya bi ta Links ɗin mu...

    𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

    https://chat.whatsapp.com/Du5LNx31U9hDi6RƘbbrzgW

    𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

    Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

    𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

    https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi

    ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

    **************************

    Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

    Question and Answers in Islam

    No comments:

    Post a Comment

    ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.

    HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.