HUKUNCIN TSEFE KAI GA MACE MAI WANKAN HAILA KO JANABA

    𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

    Assalamu Alaikum malam, da fatan kowa ya tashi lafiya, malam dan Allah ina so a yi mana bayani a kan wankan janaba da na haila, an ce idan za mu yi wankan haila sai mun tsefe kanmu, to malam dan Allah muna son karin bayani.

    𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

    Wa'alaikumus Salám. Tsefe gashin kai ga mace idan za ta yi wankan haila ko wankan janaba ba dole ba ne, idan mace za ta yi wankan haila ko na janaba, abin da za ta yi shi ne ta kamfaci ruwa sau uku ta kwarara a kanta, da zaran ruwan nan ya tsima kanta shi kenan, dalili a kan haka su ne:

    1. Sayyida Ummu Salamata Allah ya ƙara mata yarda ta ce: ya Manzon Allah ni mace ce da nake ɗaure gashin kaina, shin zan warware shi don wankan janaba da haila? Sai ya ce: "A'a. Kawai ya isar maki ki kamfaci ruwa ki kwarara a kanki sau uku, sai ki sheƙa ruwa a jikinki ki yi tsarki".

    Sahihu Muslim (330).

    2. Ubaidu ɗan Umairu ya ruwaito cewa: Labari ya iske Nana Aisha Allah ya ƙara mata yarda cewa Abdullahi ɗan Amru yana umurtan mata da su warware gashin kansu kafin su yi wankan tsarki. Sai ta ce: Abin mamaki ga ɗan Amru, yana umurtan mata da su warware kansu idan za su yi wanka. Don me bai sa su aske kan nasu ba? "Haƙiƙa Ni na kasance ina yin wanka a langa ɗaya tare da Manzon Allah ﷺ. Ba na ƙara komai a bisa kwarara ruwa a kaina sau uku".

    Sahihu Muslim (331)

    A nan Nana Aisha Allah ya ƙara mata yarda tana nufin inda ace warware gashin kai dole ne idan za a yi wankan tsarki, to da Manzon Allah ﷺ ba zai gan ta ta yi wanka ba tare da ta waraware gashin kanta kuma ya ƙi yi mata magana ba.

    A bisa waɗannan dalilai sai ya zama ba dole ne idan mace za ta yi wankan tsarki na haila ko na janaba sai ta warware kanta ba. Sai dai kawai wasu malaman sun ce idan nau'in kitson da ta yi ba zai bar ruwa ya tsuma fatar kan nata ba, to an so ta warware kan saboda wannan dalilin.

    Allah S.W.T ne mafi sani.

    Jamilu Ibrahim Sarki, Zaria.

    Zauren Tambaya Da Amsa Abisa Alkur'ani Da Sunnah. Ga Masu Buƙatar Shiga Wannan Group Za ku iya bi ta Links ɗin mu...

    𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

    https://chat.whatsapp.com/J1hm5Tw12uYBƙfaiPwf28l

    𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

    Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

    𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

    https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi.

    ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

    **************************

    Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

    Question and Answers in Islam

    No comments:

    Post a Comment

    ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.

    HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.