Igiya Nawa Ne Ya Rage Wa Mijin Da Ya Sake Auren Matar Da Ya Saki Bayan Ta Auri Waninsa ?

    𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

    السلام عليكم ورحمة الله وبركاته يا معلم كيف الحال وكيف الأسرة ما شاء الله شكرا.

    Idan mace mijinta ya sake ta saki 2 ta fita ta yi wani auren can ma aka sake ta, to sai ta dawo gidan tsohon mijinta, me saki 2 ɗin nan, ya matsayin sakin da ya yimata guda 2 a baya? Kuma na gode malam.

    𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

    وعليكم السلام ورحمة الله وبركاته. الحمد لله، ونحن بخير، وجزاكن الله خيرا.

    Matar da mijinta ya sake ta saki biyu, lokacin da ta gama idda sai wani ya aure ta, daga baya shi ma ya sake ta, ko ya rasu, sai mijin can na farko ya dawo ya ƙara aurenta, to a yanzu igiyar aurenta da mijin farkon can ya zama saura igiya ɗaya ne ba uku ba, auren ta da miji na biyu ya yi ba shi da tasiri wurin canja lissafin igiyoyin aurenta da miji na farko, kamar yadda malamai suka bayyana.

    Idan kuma lokacin da mijinta na farko ya sake ta igiyoyin aurensu dama sun ƙare, wato saki uku sun ƙare, to bayan ta auri miji na biyu, idan ya sake ta kuma ta gama idda, ko ya rasu, to a wannan yanayi idan mijinta na farko ya sake auren ta, igiyoyin aurensu za su zama guda uku ne cif, wato ta zama tamkar wacce bai taɓa auren ta ba kenan.

    Don neman daɗin bayani a duba Almugniy (7/504, 506), ko a duba Assharhu Almumti'u Ala Zádil Mustaƙni'i (13/197).

    Allah S.W.T ne mafi sani.

    Jamilu Ibrahim Sarki, Zaria.

    Ga Masu Buƙatar Shiga Wannan Group Zaku iya bi ta Links ɗin mu...

    𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

    https://chat.whatsapp.com/JLojawdOWYsEOeSHZMNdjf

    𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

    Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

    𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

    https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi

    ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

    **************************

    Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

    Question and Answers in Islam

    No comments:

    Post a Comment

    ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.

    HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.