Kishi Rahama Ne Ko Azaba //01

    MA'ANAR KISHI

    Kishi wata kalma ce ta Hausa dake nuna  abin da mutum ko waninsa ke ciki na son abu da Æ™oÆ™arin kare shi ta hanya mai kyau ko mummuna. In za a fadada za a iya cewa kishi wasu tunane-tunane ne da mutum ke yi waÉ—anda ke bayyana a fuskarsa ko mu'amalolinsa, ko ma a maganganunsa yayin da da yake zaton cewa akwai wani a kusa wanda yake Æ™oÆ™arin hambare gwamnatinsa a daidai lokacin da yake matuÆ™ar son wani abu, ko da kuwa shi wancan din ya san da halin da wannan yake ciki ko bai sani ba.

    Kishi a wurin Bahaushe kai tsaye kan rabu zuwa gida biyu ne, sai dai kowanne da dalilinsa:-

    1) Akwai kishi mai kyau, wanda ake kwadaitar da mutum ya yi, galibi yana nuna tattali ne da son kariya, kamar kishin ƙasa ko na al'umma, ko miji ya yi kishin matarsa ta wurin gyara suturta, muryarta, jikinta ko ma mutuncinta, ya killace ta sai dai shi kadai, ko mace ta yi kishin mijinta ta wurinta kare sirrinsa da sirrin gidansa. Wannan kam abin zargi ne ma in mutum bai sifantu da shi ba, yakan kuma zama abin magana ga kowa.

    2) Akwai kishi mummuna wanda galibinsa son kai ne zalla, mutum kan rufe idonsa ya ƙi gane duk wata gaskiya matuƙar ba za a bar masa abu shi kadai ne ba. Wannan kam abin zargi ne ko da kuwa a tsakanin ma'aurata ne, wato: A maza dai akan sami namijin da zai yi mummunan kishin da hujjar bai son ya rasa ne. A mata kuwa mace kan yi ne hujjar tsoro galibi, ko da kuwa ita ce mai ƙarfin.

    Ba yadda za a iya cewa kishin namiji ko mace abu ne mai kyau ko mummuna sai an san haÆ™iÆ™aninsa, in na ba da kariya ne ta hanya mai kyau wannan kam abin yabo ne, in ya fito na son kai yadda mutum zai nuna shi kadai yake son ya mori abu wannan kam mummuna ne, amma komai yana da dalilinsa, wani lokacin abu kan bayyana mummuna ne amma in aka lura da dalilinsa sai ya yi bakan-zata. Ba duka kishi ne kyakkyawa ba, haka ba kowanne ne za a watsar ba,  abin da muke so wannan dan littafi ya karanta ke nan a wannan lokacin.

    Wai da gaske ne kishin da mace ke yi a gida na ƙiyayya da duk wata matar da shiga rayuwar mijinta ko da ba tare za su zauna a gida daya ba tsabar ƙauna ne ga maigida ko tsoro ne na kar ta rasa falalar da da take samu a wurin maigidan? Ko tana jin cewa ne amaryar za ta saka ta yin wasu abubuwan da da a baya ba ta yi? Ko kuma gudun kar amaryar ta kore ta ne a gidan? Ko ba ta son a raba komai ne biyu ita kadai take? Wasu dai a bayyane suke, wasu kuma Allah kadai ya bar wa kansa sani.

    Amma mun sani wace za ta shigo ba cewa take wa uwargidan fita ki bar min gidan ni ma na dana ba, akan sami taÆ™addama ne a tsakaninsu, a Æ™arshe shi maigidan ne alÆ™ali, kuma a hannunsa ne auren kowa yake, kodai amaryar ta bar gidan don Æ™ashin kanta in taga azaba ta yi yawa, ko uwargidar ta kama gabanta da izinin wanda ya kawo ta saboda ya ga Allah a zuciyarta.  abin da babu shakka a ciki da yawa amaren kan yi shakkun uwargida, masamman in sun ji dabi'unta ba abin a yaba ba ne, wasu ma sukan fasa auren. Wasu lokutan kuma uwayen gidan ne kan ta da hankulansu saboda tsoron waÉ—anda za su shigo, masamman in amaren ba yara ba ne, ko kuma waÉ—anda idanunsu ya bude ne, ko wasu Æ™abilu ne da suka yi suna a wani fanni na rayuwa wanda ita uwargidan take ganin za a bar ta a baya.

    Bisa ga wannan dan bayani za a fahimci cewa kishi na tattare ne da mummunan zato wanda ake yanke hukunci a kan  abin da bai da tabbas don cimma buri. Kishi dai halittaccen lamari ne ga namiji ko mace. In ya yi muni yakan kai ga yin kisa a kowani bangare, namiji kan iya kashe abokin karawarsa don samun  abin da yake nema. Mace ma kan iya kashe wata don ta zauna ita kadai ko ta kai ga kwanciyar hankalin da take zato. ko da yake mafi yawancin lokuta  abin da mata ke fadi ba su ne ainihin dalilan ba.

    Duk muna sa rai bayani zai zo sanka-sanka sai dai akwai kishin da in mutum ya yi yakan fasa ne kowa ya rasa. Wani kuwa yakan haÆ™ura ne da abu duk tsananin buÆ™atarsa da shi, wani yakan fara bibiyar mafita ne, tare da sa rai da samun nasara. Wani kuwa kan gwammace ya yi abida zai iya zama ajalinsa, da dai ya bari wani ya yi tarayya da shi a  abin da yake zaton a hannunsa yake kuma nasa ne shi kadai. To in haka ne wasu abubuwan ne ke motsa wa mutane kishinsu?

    Anan Zan Dakata Sai Mun HaÉ—u a Rubutu Na Gaba.

    **************************
    Daga:  Baban Manar AlÆ™asim
    **************************

    Wannan É—aya ne daga cikin rubuce-rubuce da ke cike da faÉ—akarwa da ilimantarwa, waÉ—anda ake samarwa daga Zauren Markazus Sunnah. Ku bibiye su a kafafensu na sada zumunta domin samun Æ™arin bayani. Amsoshi ba ta da haƙƙin mallakar waÉ—annan rubuce-rubuce, amma tana É—ora su ne da izinin Baban Manar AlÆ™asim.

    Kishi Rahama Ne Ko Azaba

    No comments:

    Post a Comment

    ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.

    HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.