Kishi Rahama Ne Ko Azaba //02

    ME KE KAWO KISHI?

    Domin amsa wannan tambayar dole sai an raba kishin zuwa gida biyu: Mai amfani da maras amfani:

    a) Za a iya cewa akwai wasu 'yan dalilai dake kawo kishi mai amfani kamar:

    i) Ƙauna: Sonka da abu zai iya saka wa ka miÆ™e tsaye wajen tabbatar da shi, domin kana da masaniyar cewa digirgire da shi zai iya kawo tintsirewarsa don haka za ka iya amfani da harshe da harsashi wajen ganin ba  abin da ya ba ta shi. Duk lokacin da wani ya gigi wurinsa da wata manufa za ka yi tsayuwar daka don kubutar da shi don shi ke ranka kuma shi kake Æ™auna.

    Muslunci bai hana wannan ba, sai ma ƙarfafa shi ya yi, duk namijin da bai kishin iyalinsa, ma'ana bai ba su kariya ta fannin da mummunan abu ba zai shafe su ba to ba namiji ba ne, daga cikin waɗanda aka haramta musu aljanna akwai wanda bai iya tsare iyalinsa. Da wannan kishin mutum ga iyalinsa yake nuna ƙaunarsa da su, kuma ya zama wajibi.

    ii) Ba su Kariya: Ƙoƙarin da mutum yake yi wurin ba wa iyalinsa kariya alama ce dake nuna ƙaunarsa gare su. Lallai ya tsare musu addininsu, da shigarsu ta sutura, ya kare su daga shedanun aljanu da mutane yadda wani ba zai yi musu maganar banza ba, ko ya kusance su da alfahasha ta kowani bangare. Wannan nuni ne ga kishin da mutum yake wa iyalinsa.

    iii) Janyo Alkhairi: Duk yadda mutum ya ga wasu sun sami alkhairi ya yi kwadayin a ce nasa ma ya samu, ko da kuwa Æ™asa ce ko mutanensa ko ma iyalinsa. MatuÆ™ar wasu can nesa za su samu to ai kaima ya dace a ce iyalinka sun rabauta. Wannan ma kishi ne amma mai kyau. A tsakanin mata in wata tana kyautata wa maigidanta wajen yi masa duk  abin da yake buÆ™ata ke ma fara, yi masa har da gyara, wannan ma kishi ne amma mai amfani.

    b) Shi kuwa kishi maras amfani yana da nasa dalilin da suka saba wa wannan, galibinsa ba da aninyar alkhairi ake yinsa ba, wata manufa ce ta daban.

    i) Ƙarancin Imani: Idan imanin mutum ya yi ƙasa don ya ta da mummunan kishi ba wani abu ba ne, duk wanda ke da imani ba zai je wajen boka ba, in har ya tafi ya yi wa bautarsa babbar illa, Sharia ta ce mutum bai da rabo a lahira in ba dace ne ya yi da rahamar Allah ba.

    In imani ya yi Æ™asa mai mummunan kishi zai iya kisa, ko dai ya kashe mijin, ko kishiya ko ma 'ya'yanta. In wurin aiki ne zai iya kashe kowa, don  abin da yake zuciyarsa mai zai sa wane ya sami kaza, wannan kawai ya isa domin ya yi kama da hassada sosai.

    ii) Yaranta ko wautar ƙuruciya: Wannan ma wani dalili dake kawo mummunan kishi, idan muka ce yaranta ba ma nufin ga yaro, haka ƙuruciya ba wai ma'anar mai ƙaramin shekaru ba ne, a'a.

    Duk babban da ya aikata ayyukan da yaro ne zai yi to ya yi yaranta; kamar imani da  abin da ba zai yuwu ba, misali namiji ya ce wa matarsa ita ce tauraruwarsa Æ™wara daya a sararin samaniyarsa, ita kuma ta sani sarai taurarin dake sararin subhana Allan da ya yi su shi kadai ya san yawansu. Ba yadda namiji zai ce mace Æ™waya daya ce a zuciyarsa bayan Allah SW ya ba shi damar da zai so mata da yawa a zuciyarsa. Irin wannan yarda ke sakawa ta amince wa kanta to ita kadai ce, duk lokacin da ya fara son wata sai ta ga cewa ita ce ke Æ™oÆ™arin shiga mata rayuwa, alhali amincewar da ta yi ta ba zai so wata ba ta jawo mata.

    Maganin irin wannan kishin rashin saka wa kai cewa maigida ya kulle ƙofa ke nan wata ba za ta shigo ba, bayan ke kina cikin gidan ne shi kuma kullum yana waje, kuma matan ga sunan kala-kala a waje. Wace ta yi imani da cewa maigidanta zai iya ƙara aure to ko ya yi maganar auren ba zai zama sabon abu a wurinta ba. Abu ne da ta sani cewa zai iya faruwa, kuma in ta yi ƙoƙarin hana shi yin abida ya riga ya yi niyya to sai dai cikin biyu a yi daya: Kodai ta haƙura akan dole ya yi auren da ya yi niyya, ko kuma ta kama gabanta amaryar ta zauna a dakinta.

    Anan Zan Dakata Sai Mun HaÉ—u a Rubutu Na Gaba.

    **************************
    Daga:  Baban Manar AlÆ™asim
    **************************

    Wannan É—aya ne daga cikin rubuce-rubuce da ke cike da faÉ—akarwa da ilimantarwa, waÉ—anda ake samarwa daga Zauren Markazus Sunnah. Ku bibiye su a kafafensu na sada zumunta domin samun Æ™arin bayani. Amsoshi ba ta da haƙƙin mallakar waÉ—annan rubuce-rubuce, amma tana É—ora su ne da izinin Baban Manar AlÆ™asim.

    Kishi Rahama Ne Ko Azaba

    No comments:

    Post a Comment

    ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.

    HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.