Kishi Rahama Ne Ko Azaba //11

    6) AZABA A LAHIRA: A duniya dai akan kau da kai a kan duk  abin da mace ke yi da sunan kishi, sau tari ba wani mataki kuma da ake dauka, hakan ta sa masu kishin suka sami damar bin mazansu har tsakiyar kasuwa su zazzage shi su koma gida su yi zamansu ba  abin da zai faru. Na ga wace ta fasa wa maigidanta babban gilashin mota na baya kuma ba  abin da ya yi. Wata ta Æ™ona kayansa gaba daya kuma aka zauna lafiya wai kishi ne.

    Wata kuwa kekketa shi ta yi da wuƙa kuma ya zuba mata ido wai uwar 'ya'yansa. Na yi hira da wace ta ce kishiyar mamansu ta zuba musu kalanzir ƙyasta wutan ne kawai ba ta yi ba Allah ya ƙwace su. Akwai matan da suka kashe kansu don kishi, to ko wannan Allah ba zai yafe ba bare wanda ta yi wa wani ƙeta. Na ga matar da ta riƙa kwasan kayan mutane tana saka wa kishiyarta don a zarge ta da sata. Wata ta riƙa ƙala wa kishiyar wai tana zuwa neman maza. In aka ce kishi ne shi kenan.

    Amma fa ba iyakarta ke nan ba, mutane za su iya mantawa, shi kuwa mahaliccinsu ba zai yafe ba. Ko bai bi musu kadi anan duniya ba akwai ranar hisabi, babbar matsalar kishi ba a iya roƙon kishiya ta yafe sai an hadu a lahira. Misali wace ta raba wata da mijinta ko da boka ko da kisisina hisabinta daban ne a wurin Allah, wanda galibin mata masu kishi ba su da buri kamar matar da aka auro ta saku, ko ita da shigo daga baya ta fitar da ta cikin, ba tare da sanin irin azabar da za ta hadu da ita a lahira dalilin hakan ba.

    Hadisin Jabir wanda Muslim ya rawaito ya ce: "Shedan kan dora gadon mulkinsa a kan ruwa ya tura 'yan kanzaginsa, fitinannun ne fadawansa na kusa: wani zai zo ya ce "Ai na yi kaza da kaza" ya ce "Ba ka yi komai ba" sai wani ya zo ya ce "Ai ban bar shi ba sai da na raba shi da iyalansa" sai ya jawo shi kusa ya ce "Yauwa! Kai ka yi abin yabo". To ta ya za ki raba mutum da matarsa ba ki yi tunanin kin zama daya daga cikin fadawansa na kusa ba? Ai kina cikin shedanun mutane.

    Wace za ta daga murya tana zagin kishiyarta ba tare da ta yi mata komai ba, a dole ita kishi ne take yi, ai ta shiga cikin waɗanda Allah SW ya fada a Suratul Ahzab cewa sun ja wa kansu laifi da zunubi bayyananne. ke nan za a hadu da Allan, to bare kuma masu yi wa kishiya ƙazafi, ko hassada dake cinye kyawawan aikin mutum, abin tsoron hassadar ta fi ƙarfi a tsakanin kiyoshi. Ba sa ƙaunar ganin kishiyar da alkhairi, ko kuma ta yi ta burin arziƙin da ta samu ya gushe.

    Wani zunubi ne mafi girma kamar zuwa wurin boka da sunan an je karbo taimako? Ko an tashi a tsaye don kare kai? Da yawa mata kan fake da cewa sun je neman taimako ne don kare kai daga kishiya, alhali tsafi ne dake shigar da mutum wuta. Akwai wace za ta ce a hana wata haihuwa gaba daya sai dai ita, ga laifin zuwa wurin boka ga na barnar da za a yi wa kishiya wanda ba yadda za a yi sai in ita kishiyar ta yafe.

    Duk wata matsalar da za a tura wa kishiya an yi aiki da aljani ne, wanda ta sani ga shinan a Ƙur'ani Æ™arara Suratul BaÆ™ara mai yin hakan ba ta da rabo a lahira, an yi tir da  abin da take aikatawa. A taÆ™aice dai bayan matsalolin kishi da mace kan fuskanta a a zamantakewarta ta duniya da mutanen dake kewaye da ita, ko a lahirar ma wasu matsalolin ne na daban. Don kuwa Allah SW ba zai bari ya wuce haka kurum ba.

    To macen da ta je yi wa kishiyarta mugunta ya dawo kanta Allah SW ba zai yafe ba bare wance ta yi din kuma ya kama kishiyar? Ina jin wata malama na magana take cewa galibinmu kishi ke kai mu wuta, tunda ba kalar sabon Allan da ba ma yi a kansa, ta ce abin takaicin ba wani dadi muke ji ba in mun yi, ba kuma wani darasin da muke dauka in ya rikice wa wata. Maganar sakamakon duniya da lahira duk mun sani amma ba ma yin la'asar. Malaman cikimmu ba su tsira ba bare waÉ—anda ba su dauki shari'a a matsayin magwaji ba.

    Anan Zan Dakata Sai Mun HaÉ—u a Rubutu Na Gaba.

    **************************
    Daga:  Baban Manar AlÆ™asim
    **************************

    Wannan É—aya ne daga cikin rubuce-rubuce da ke cike da faÉ—akarwa da ilimantarwa, waÉ—anda ake samarwa daga Zauren Markazus Sunnah. Ku bibiye su a kafafensu na sada zumunta domin samun Æ™arin bayani. Amsoshi ba ta da haƙƙin mallakar waÉ—annan rubuce-rubuce, amma tana É—ora su ne da izinin Baban Manar AlÆ™asim.

    Kishi Rahama Ne Ko Azaba

    No comments:

    Post a Comment

    ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.

    HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.