MAFI YAWAN MATA 'YAN WUTA NE

    DALILI NA 5

    *****

    Daga cikin abinda yake jawowa mata shiga wuta shi ne bayyana tsiraici, tsiraici kuwa shi ne bayyana abinda ALLAH TA'ALAH ya yi umarni a suturce na ado kyau in ba ga muharrami ba.

     Manzon ALLAH {s.a.w} yana cewa: Nau'o'i biyu daga '‘yan wuta ban gansu ba, sun nutse a wuta.

     Wasu mutane masu bulalu kamar jelar saniya suna dukan mutane dasu.

     Da wasu mataye masu tufafi, amma haƙiƙa matsiraita ne, karkatattu masu karkatarwa, kawunansu kamar toron raƙumi, ba za su shiga aljannah ba, bama za suji ƙamshin ta ba, kamar anajin ƙamshinta daga tafiyar kaza da kaza.

    Wannan hadisin yakawoababe guda biyu dake jefa mata wuta, wato shiga ta tsiraici, da kuma wani da akeyi da gashi a ƙeya ya yi tudu, (wato acuci) wannan acucin shima yana kai mace ga shiga wuta.

     Umayyatu '‘yar Rafikatu ta zo wajen Manzon ALLAH {s.a.w} tana yi masa mubaya'a akan musulunci,

    Sai ya ce:

    Zanyi mubaya dake akan ba zakiyi shirka da ALLAH ba, ba zakiyi sata ba, ba za kiyi zina ba, ba zaki kashe ɗanki ba don tsoron talauci, ba za ki zo da wata ɓarna ba, da zaki ƙirƙireta da hannunki ba, ba zakiyi kururuwar mutuwa ba, ba zakiyi tsiraici irin tsiraicin jahiliyyar farko ba.

    [Ahmd ne ya rawaito shi]

    Lura da yadda Manzon ALLAH {s.a.w} ya haɗa tsiraici da manyan laifuka irinsu shirka da zina da sata, to lallai saka kaya masu matse jiki wanda suke nuna komai na jikin mace, wanda suke kama jikinta yana kaita ga shiga wuta.

     Haka kuma kururuwa da mata keyi idan akayi mutuwa suyita ihu sunata kuka, watama tana faɗuwa ana ɗaukarta, wata kuwa tana suma, wannan shima yana jawowa meyinsa shiga wutar ALLAH.

     Bayyana tsiraici kuwa ya haɗo da saka turare mai ƙarfi a fito waje, ko man shafawa mai ƙamshi a fito waje, sai kuma saka kaya masu bin jiki, masu fito da surar mace ko da kuwa masu kauri ne, da kuma kaya masu shara-shara.

     Manzon ALLAH {s.a.w} ya ce: Duk sanda mace ta saka turare ta fita wajen mutane don aji ƙamshinsa, to ita mazinaciya ce ga kowanne ido daya ganta.

    Ma'ana duk wanda yaganta za a rubuta mata laifin zina, ga duk mutum ɗaya daya kalleta.

     Shigar banza, saka kaya masu kama jiki, masu fito da surar mace suna jawo mata tsinuwar ALLAH kuma suna jawo mata shiga wutar ALLAH.

     Haka kuma yin acuci da gashi wato a cure gashin a ƙeya ya yi wani tudu shima wannan yana kai mace ga shiga cikin jahannama.

     Ina kira gareku mata da kuji tsoron ALLAH ku kiyaye saka kayan da suke bayyana surarku domin duk mai irin wannan zata haɗu da ALLAH yana mai fushi da ita, kuma sakamakonta ita ce wutar jahannama.

    ALLAH ka bamu ikon aiki da abinda muka karanta.

    ALLAH ka yafe mana zunubanmu baki ɗayanmu Ameen.

     ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

    **************************

    Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

    Question and Answers in Islam

    No comments:

    Post a Comment

    ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.

    HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.