Tsaro a Matakin Hukuma: Hukuma Da Mahukunta a Zamfara 2015-2019

    This article is published in the Tasambo Journal of Language, Literature, and Culture – Volume 1, Issue 1.

    Musa Abdullahi
    08037765415

    Isah Sarkin Fada
    08039165872

    Department of Languages and Cultures, Federal University Gusau, Zamfara State, Nigeria

    Tsakure

    Hukuma (wato abin nufi a nan ita ce gwamnati) ita ce Æ™ashin bayan al’umma a duniya, domin duk Æ™asar da ba ta da hukuma da ke kula da tsarin rayuwarta da al’amuran harkokinta na yau da kullum; ta kauce hanya. Haka kuma wannan Æ™asa ko gari za a iya cewa sun taÉ“e sun shiga ruÉ—u na rashin sanin alÆ™iblar da suka dosa. Wannan bincike zai yi tsokaci ne kan irin gudummuwar da hukumar jihar Zamfara ke bayarwa wajen kula da tabbatar da tsaro da ya shafi mutane ko al’ummar da ke cikin jihar, dangane da irin faÉ—ace-faÉ—acen da ke faruwa tsakanin makiyaya da manoma. Wannan hali ya haifar da matsalolo iri-iri ta hanyar kashe-kashen rayuka, ta’addanci da garkuwa da mutane don karÉ“ar kuÉ—in fansa ya zama ruwan dare. Hukuma ta bayar da gudummuwa don ganin ta warware waÉ—annan matsalolin da suka addabi jama’a ta hanyar kafa kwamitin kulawa da harkan tsaro a jihar, wanda ya samar da hanyoyi da dama da za a bi a magance waÉ—annan matsaloli da suka bijiro a wannan jihar ta Zamfara.      

    Gabatarwa

    Jihar Zamfara, tana É—aya daga cikin jihohin da ke yankin arewacin Nijeriya wanda Allah ya albarkace ta da Æ™asar noma mai kyau, domin duk abin da aka shuka a Æ™asar zai fito kuma ya bayar da yabanya sosai. Saboda haka, suke alfahari da noma ga kuma kiwon dabbobi irin su Shanu da Tumaki da Raguna da dai sauran duk nau’in dabbobin da ake kiwatawa. Shi ya sa suke amfani da taken cewa “Noma shi ne alfaharinmu.” Idan aka duba da kyau lallai kuwa abin haka yake Æ™warai.

    An fara samun rashin jituwa a tsakanin al’ummomi biyu, wato manoma da makiyaya (Fulani) wajen mu’amala da juna dangane da sana’arsu na noma da kiwo game da Æ™orafin da manoma suke yi cewa, makiyaya suna cinye masu amfanin gona ta hanyar tura dabbobinsu cikin gonaki suna yin É“arna, yin haka na jawo masu hasarar amfanin gona Æ™warai da gaske.

    ÆŠaya É“angaren kuma na makiyaya suka ce ai ba da gangan suke yi ba, hakan na faruwa ne domin manoma sun cinye hanyoyi (burtali) da dabbobi za su bi su wuce zuwa kiwo a dazuka, duk sun mai da su gonakinsu. Haka dai sa-in-sa yai ta faruwa tsakanin manoma da makiyaya wanda har ya kai suka fara faÉ—a da kashe-kashen juna, nan da nan Hukuma (Gwamnati) ta miÆ™e tsaye ta shiga tsakani don kawo mafita da sulhu saboda a zauna lafiya. Hukuma ta bi ta hanyoyi da dama wajen warware matsalolin kamar ta hanyar shari’a da yanke hukunci duk wanda ya yi wa É—aya É“arna sai ya biya kuÉ—in tara, haka kuma da Æ™oÆ™arin fitar da hanyoyi (burtali) da makiyaya suke kuka a kan cewa, manoma sun cinye wato sun haÉ—e da gonakinsu ba hanyar wucewa.

    Haka dai abu yai ta faruwa, hukuma (gwamnati) tana kula da tabbatar da cewa an zauna lafiya domin ci gaban rayuwar mutanenta.

    Dalilin Bincike

    Ganin irin tarin matsalolin da ke Æ™unshe ko tattare da É—an Adam, inda ake cewa “É—an Adam mai wuyan gane hali,” duk Æ™oÆ™ari da gwamnati take yi na kawo tsaro da kulawa ga al’umma ta hanyoyi da yawa, can kuma sai a ga wata matsalar ta fito, wannan ya ba mu damar yin bincike domin gano ire-iren hanyoyin da hukuma take bi don murÆ™ushe ko samar da mafita da tabbatar da tsaro a jihar Zamfara.

    Farfajiyar Bincike

    Wannan bincike zai dubi irin gudummuwar da hukuma ke bayarwa wajen tabbatar da tsaro a jihar Zamfara wanda ya shafi ire-iren matsalolin ta’addanci na harbe-harben mutane babu dalili da masu garkuwa da mutane don karÉ“an kuÉ—in fansa da rashin jituwa tsakanin manoma da makiyaya a jihar Zamfara.

    Dabarun Bincike

    Binciken ya yi amfani da bayanai da tsare-tsaren da hukuma (gwamnati) ta tanadar wajen tabbatar da cin nasarar samar da zaman lafiya tare da kafa kwamitin kulawa da harkan tsaro, inda aka samu damar zantawa da wasu wakilan gwamnati masu ruwa da tsaki a wannan gwamnati mai ci, irin su Kwamishinan Tsaro da Harkokin Cikin Gida da Shugaban Kwamitin Tsaro na Jihar Zamfara da Sakataren ‘Yan Sa Kai a shekarar, 2019. Bayan haka, an duba hanyoyi da tsare-tsaren da aka tanada wajen samar da maslaha ga dukkanin matsalolin da ke faruwa.

    Matashiya

    Hukuma: Jama’a ce ko mutane ne da ke kula da tsarin tafiyar da mulki ko jagorancin Æ™asa tafarkin da aka tsara ko turban da aka kafa Æ™asar domin kiyayewa da tafiyar da dokokin tsarin mulkin da aka kafa, aka amince da bin su a Æ™asar. Wannan ya sa Bahaushe ke cewa, “Hukuma sai lallashi,” saboda ita hukuma na zartar da hukunci ne ga duk wanda ya taka doka ko wane ne shi a cikin Æ™asa wanda ya yi daidai da irin laifin da mutum ya aikata. Idan aka kiyaye doka sai a zauna lafiya. Bunza (2015).

    Tsaro: Wannan hanya ce da ake bi domin kulawa da Æ™asa da dukiyarta da mutanen da ke cikin Æ™asar, saboda gujewa É“arna da cin mutuncin al’umma. Tsaron Æ™asa mutane ke yin sa, rashin tsaro daga ayyuka da halayen mutane yake. Bahaushe na da tsarin tsaro cikin tsarin sarautarsa ta gargajiya inda yake tafiyar da al’amuransa cikin sauÆ™i tattare da hukunci mai kyau Shehu (2018).

    Da tafiya ta yi tafiya, sai darajar sarautun gargajiya ya fara dusashewa, ginshiƙin tsarin kula da gudanarwa ya yi baya, sai aka dasa wayewar ci gaban mai gina rijiya, abubuwan da suka jawo hakan sun wanzar da rashin tsaro na har abada akwai:

    i)        Mulkin mallaka

    ii)      Siyasa

    iii)    Boko

    iv)    Kutsen baÆ™in al’adu

    Su suka fara wargaza sarakunanmu na gargajiya da naÉ—a irin nasu masu biyayya ga al’adunsu. TuÉ“e Sarki da naÉ—a shi ya zama wasan yara. Kashe Sarki da tura shi gudun hijira ya zama ruwan dare. Miyagun É—abi’unsu na shaye-shaye da suturar tsiraici da sauran munanan abubuwa waÉ—anda ba a san Bahaushe ko al’ummar Hausawa da su ba ya zama sun karÉ“e su sun yi katutu a rayuwarsu ta yau da kullum. Bunza (2018).

    Gudummuwar Hukuma kan Tsaro

    Hukumar jihar Zamfara (gwamnati) ta yi ruwa ta yi tsaki don kawo Æ™arshen matsalolin da ke addaban jihar na ta’addanci iri daban-daban na siyasa da rikicin makiyaya da manoma da satar mutane da garkuwa da su da saka masu kuÉ—in fansa, ga masifar fyaÉ—en yara maza da mata sun zama ruwan dare, ga tsaface-tsaface na burin tara abin duniya da mallakarta. A tarihin duniyar mutane, babu Æ™asar da za ta samu kanta cikiin ire-iren waÉ—annan matsaloli face sai ta durÆ™ushe. Shawo kan irin waÉ—annan matsaloli sai an yi da gaske matuÆ™a. Atuwo (2009) da Bunza (2018).

    Haka ya sa hukuma (gwamnati) ta jihar Zamfara ta kawo É—auki na gaggawa domin shawo kan matsalolin ta hanyoyi kamar haka:

    1.       NaÉ—a Kwamishinan Tsaro da Kula da Harkokin Cikin Gida

    2.       NaÉ—a Kwamitin Kulawa da Harkar Tsaro.

    3.       Samar da isassun jami’an tsaro tare da makamai.

    4.       Samar da kuÉ—aÉ—e domin gudanar da harkar tsaro.

    5.       Samar da ayyuka ga matasa.

    6.       Samar da guraben karatu ga matasa.

    7.       Samar da hanyar sulhu tsakanin gwamnati da ‘yan ta’adda da kuma masu garkuwa da mutane.

    8.       Samar da hanyoyin tattaunawa da sarakuna iyayen Æ™asa masu jagorantar al’umma, don samun mafita.

    9.       Sa ido da hana haÆ™ar ma’adanai a Æ™asar.

    Duk waÉ—annan gwamnati ta samar da su ne domin samun mafita game da yanayin da ake ciki; don samar da zaman lafiya mai É—orewa. Abubakar (2020).

    Mulki da Tsaro

    Masana sun yi magana dangane da yadda tsarin mulki ke wanzuwa a tsakanin al’umma kamar inda Acemoglu da Wasu (2013) suka ce: Mulki, abu ne da ke son kulawa da zartar da gaskiya wajen gudanar da shi a kan waÉ—anda ake mulka don samun yin adalci a tsakani. Haka kuma, mulki ba zai tafi ba shi kaÉ—ai sai da tsaro da kiyaye abubuwan da suke kai-komo a cikin al’ummar da ake mulka, saboda gujewa taÉ“arÉ“arewar rayuwa irin na halaye kamar haka:

    i)        Yawaitar cin hanci da rashawa.

    ii)      Bazuwar kangararrun yara a ko’ina.

    iii)    Ta’addanci da sauran laifuka.

    iv)    Shaye-shaye ga matasa.

    v)      Rashin shugabanni nagari.

    Doka a Kadadar Adabi da Al’ada

    Doka da hukunci suna tafiya ne a tare don cim ma manufa, ba abin da za a saka wa mutane kai tsaye da rana tsaka ba ne, ana tanadin shi ne tuntuni kafin a sami matsala. Cikin adabi da al’adun al’umma za a tsinci dokoki da ke tattare da rayuwarsu. Haka kuma, za a dinga kiyayewa da su da huruminta har a tarbiyantu da tsarin dokokin. Aminu (2014) da Muri (2003).

    Daga cikin nason da doka ke yi a adabi akwai karuruwan maganar da ke nuna matsayin hakan a al’adance irin su:

    i)        Bin na gaba, bin Allah.

    ii)      Kowa ya yi da kyau, zai ga da kyau.

    iii)    Mai dokar barci, ya É“uge da gyangyaÉ—i.

    iv)    Doka daga gida take farawa.

    v)      A bi doka, a zauna lafiya.

    Bin doka da kiyaye ta, ya yi tasiri a kan tarbiyyar Bahaushe sosai, saboda tsarin mulkin sarakuna na gargajiya da tun fil-azal Bahaushe yake da su a rayuwarsa na shugabanci, tun daga gida akwai daraja iyaye da bin dokokin da suka gindaya wa kowa a cikin gida. Haka kuma, ga masu unguwanni a ƙauyuka da dagatan kowane yanki da kuma sarakuna a duk ƙasashen Hausa.

    Duk abubuwan da aka tsara game da tsarin rayuwar mutane, haka za a bi a kiyaye su domin a cim ma nasara.

    Sakamakon Bincike

    Binciken wannan takarda game da “Matakin Hukuma Wajen Kula da Tabbatar da Tsaro a Jihar Zamfara.” An auna irin rayuwar da hukuma (gwamnati) ta taka wajen tabbatar da tsaro ga Æ™asa da bunÆ™asarta. Binciken ya tabbatar da cewa matsalar tsaro ta kowa da kowa ce, domin tsaro ya shafi duk wanda ke farfajiyar da Æ™asa ta kafa tutarta. A binciken da aka gudanar an gano abubuwa kamar haka:

    i)        Ƙarfin iko da amfani da muÆ™ami duk ba su isa su tabbatar da tsaro ba, sai an yi amfani da tsarin al’adun mutanen da aka tanada wa tsaro saboda sun fi tasiri a gare su da gina tabbataccen tsaro a zamantakewarsu.

    ii)      Gina tarbiyya da tsaro don bin dokoki da aka tsara a zukatan mutane a ko’ina wanda ke da alaÆ™a da al’adunsu zai taimaka.

    iii)    Nagartaccen tsari, ba da Æ™arfin bindiga ake samar da shi ba, ana amfani da hanyar cusa wa ‘yan Æ™asa kishin bin dokar Æ™asar ne a zukatansu da wakilan tsaronsu.

    iv)    TaÉ“arÉ“arewar shugabanci a zukatan shugabanninmu da handama da babakere a kujeran mulki, sai “mutu ka raba” ya haifar da rashin tsaro.

    v)      Rashin kishi da ko-in-kula da al’adunmu da É—abi’unmu da adabinmu ya haifar da matsaloli na rashin tsaro a tsarinmu.

    NaÉ—ewa

    Tunanin Bahaushe a kan tsaro da tanadinsa, hanya ce da za a yi amfani da tsarin dokoki wanda ya Æ™unshi tsaro, ta yadda za a cusa a zukatan yara da matasa cikin adabi da wasannin gargajiya a harkokin mu’amala da juna kodayaushe. Bahaushe na cewa hannu É—aya ba ya É—aukar jinka, don haka sai duk an taru wajen bayar da goyon baya game da kula da tabbatar da tsaro a Æ™asa baki É—aya.Gwamnati jihar Zamfara ta tashi tsaye wajen samar da zaman lafiya ga al'uma. Kamar inda Musa ÆŠanÆ™wairo Maradun ya ce a waÆ™arsa kamar haka:

    Kowag gyara ya sani.

    Kwaɓ ɓata ya sani.

    DaÉ—ai mutum ba ya son.

    Mai yi mai jarfa.

    Manazarta

    1.       Acemoglu, D. and Jame, A.R (2013) Why Nations Fail the Origins of Power, Property and Poverty. London: Profile Books Ltd.

    2.       Aminu, N. (2014) “Culture in the Administration of Peace: Hausa Marriage Under Review. Paper Presented at the International Conference on Social Behaviour and Conflict management, Ghana.” University of Café Coast.

    3.       Atuwo, A.A. (2009) “Ta’addanci A Idon Bahaushe: YaÉ—uwarsa da Tasirinsa A Wasu Ƙagaggun Labaran Hausa.” Kundin Digiri na uku, Sakkwato: Jami’ar Usman ÆŠanfodiyo.

    4.       Bunza, A.M (2015) “Labarin Zuciya A Tambayi Fuska: SaÆ™on Dariya ga Sasanta Tsaro A Farfajiyar Karatun Hausa.” Takardar da aka Gabatar a Sashen Hausa, Makarantar Harsuna, Kwalejin Ilimi ta Adamu Augie, Arugungu.

    5.       Bunza, A.M (2015) “Zaman Lafiya da Tsaro a Daular Musulunci ta Sakkwato Abin Koyi ga Shugabannin Zamaninmu.” Takardar da aka Gabatar a Taron Yini ÆŠaya da Centre for Intellectual Services on Sokoto Caliphate ta Shirya, Sakkwato: Jami’ar Usman ÆŠanfodiyo.

    6.       Bunza, A.M. (2015) “Zaman Lafiya ya fi Zama É—an Sarki: Tunkarar ZaÉ“en 2015 a Nijeriya.” Takardar da aka Gabatar a Taron Kyautata Zaman Lafiya a ZaÉ“en da aka Gudanar 2015 wanda Orphans of Huffaz Educational Foundation Birnin Kebi Suka shirya.           

    7.       Bunza, A.M (2018) “Kunya GinshiÆ™in Tsaron Ƙasa da BunÆ™asarta.” Takardar da aka Gabatar a ƘarÆ™ashin Tarayyar HaÉ—aÉ—É—iyar Ƙungiyar ÆŠalibai ‘Yan Jihar Zamfara a ƘarÆ™ashin Jagorancin Kwamishinan Ilimi na Jihar Zamfara.

    8.       Muri, A.M. (2003) “The Defence Policy of the Sokoto Caliphate 1804 – 1908, Ph.D. Thesis, Sokoto: Usmanu ÆŠanfodiyo University.”

    9.       Shehu M. (2018) “Zaman Lafiya ya fi Zama ÆŠan Sarki: Tunanin Bahaushe a kan Zaman Lafiya da Sasantawa.” Kundin Digiri na uku, Sakkwato: Jami’ar Usmanu ÆŠanfodiyo.

    DOI: https://dx.doi.org/10.36349/tjllc.2022.v01i01.020 

    Click HERE to download the complete article.

    Tasambo Journal of Language, Literature, and Culture

    No comments:

    Post a Comment

    ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.

    HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.