Juyin Waina

    Matarsa ta ce: “Kwana biyu na rabu da ganin abokinka Abdul a gidan nan, Allah ya sa dai lafiya.”

    Sai ya ce “Mun ɗan samu saɓani da shi kwana biyu, amma za mu shirya.”

    Sai ta ce “Allah Sarki! Abdul mutumin kirki na san yanzu haka laifinka ne, ƙila kai ne ka ɓata mishi rai.”

    Sai ya ce “ A'a ko kaɗan! Ce mishi na yi ina so in sayi mota da ƙuɗin da na samu a siyasar bana, shi kuma yake bani shawarar wai aure yakamata in ƙara tun da na samu dama,

    Na nuna ƙin amincewa ta da shawararshi, shi kuma ya ji haushi ya ce kwata-kwata ba na son ɗaukar shawararshi, tun daga nan ko na kira a waya ba ya ɗauka.”

    Sai ta ce “ Ƙyale ɗan banza!, Ni fa da ma kaf a cikin abokanka sam ban yarda da wannan mai ruwan munafukan ba.”🤣

    Juyin Waina

    No comments:

    Post a Comment

    ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.

    HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.