Kashles - Ta Malam Khalid Imam

    Wannan na ɗaya daga cikin jerin waƙoƙin Malam Khalid Imam da a kullum suke faɗakarwa da ilimantarwa da nishaɗantarwa. Yana taɓo fannoni daban-daban a cikin waƙoƙinsa, ciki har da abubuwan da suka shafi lamuran yau da kullum.


    Allah Ke 'yanta kowa,

    Nairarmu da da a baya,

    Mu ke liƙi mu taka,

    Muna ta rawa a kanta,

    Allah Ya ba ta 'yanci,

    Ba mai liƙata yanzu,

    Ya taka rawa a kanta.


    Allah Ya 'yanta Naira,

    Nairar da mu da kanmu,

    Mu kewa cin mutumci,

    Mai man ja duk da man jan,

    Bai goge hannuwansa,

    Yake shakar wuyanta,

    Haka ma mai saida ƙosai.


    Da kwandasta na mota,

    Da mai gyara na babur

    Suna murÉ—e wuyanta,

    Ba wanda ya damu da can,

    Maza mata da yara,

    Ya tsare haƙƙi mutunci,

    Na Naira sai ƙalilan.


    Kashiles ya zo ƙasarmu,

    Naira yau tai mutunci,

    Daraja ƙima a hannu,

    Layi jama'a da kansu,

    Su ke yi babu soja,

    Ko É—an sanda a banki,

    Ko kaÉ—an Naira a ba su.


    Kashiles ma na da rana,

    Duk da ya matse mutane,

    Yasa jama'a fahimtar,

    Darajar Naira a hannu,

    Masu liƙawa su taka,

    Yau babu bare su liƙa,

    Su taka rawa da homa.

    Malam Khalid Imam
    08027796140
    khalidimam2002@gmail.com

    13/3/2023

    No comments:

    Post a Comment

    ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.

    HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.