Zan Iya Auren Wacce Kishiyar Mamana Ta Shayar?

    Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

    Tambayoyi Da Amsoshi

    𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

    Aslm' alkm. Ina yiwa malam fatan alkhairi, ina tambaya ne don Allah a kan idan matar mahaifina (Yadikkona) ta shayar da wata mata a gidanmu wanda ba ƴarta ba lokacin ma ni ba a auri mamata ba, toh zan iya auren wannan matar da aka shayar a gidan mu ko ta zama ƴar ƴar'uwata. Allah Ya kara basira da kuma Ikhlasi.

    𝐀𝐌𝐒𝐀👇

    Wa alaikumus salam. Bai halatta ka aure ta ba, saboda da nonon mahaifinka aka shayar da ita, don haka ta zama 'yar'uwarka.

     

    Allah Madaukakin Sarki ya haramta auran 'yar'uwa ta fuskar shayarwa a aya ta (22) a suratun Nisa'i.

     

    Allah ne mafi sani.

     

    Dr. Jamilu Yusuf Zarewa

     

    Ku Kasance Damu Cikin Wannan Group Domin Ilimantarwa Tare Da Faɗakarwa a Sunnah.

    𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

    https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi

    𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

    Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

    𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

    https://chat.whatsapp.com/BD0aB20SWTB9hgHahFHb9M

     

    ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

    No comments:

    Post a Comment

    ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.

    HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.