Littafin Azumi [ 04 ] – Rukunnan Azumi

    RUKUNAN AZUMI

    Rukunan Azumi guda biyu ne:

    1• Niyya:

    Rukuni na farko Azumi baya yiwuwa idan babu niyya.

    Dukkanin ayyuka ba sa yiwuwa sai da niyya.

    [Bukhari da Muslim].

    2• Kamewa ga barin ci da sha.

    Rukuni na biyu daga cikin rukunan Azumi shi ne kamewa ga barin duk wani abinci ko abin sha ko jima’i.

     ALLAH TA'ALAH ya ce:

    Ku ci ku sha har izuwa ku bambance tsakanin farin zare da baƙin zare daga hasken alfijir, sannan ku cika Azumi izuwa dare.

    [Suratul Baƙara: ayata:187].

     SUNNONIN AZUMI DA LADUBBANSA

    Azumi yana da sunnoni da mustahabbai, su ne kamar haka:

    1• Sahur: Shi mustahabi ne a gamuwar malamai, wanda baiyi shi ba, ba shida laifi, sai dai wanda ya yi sahur ya fishi yawan lada.

     Domin Annabi {s.a.w} ya yi umarni da a yi Sahur.

     Daga Anas Ɗan Malik (R.A) ya ce:

     Manzon ALLAH {s.a.w} ya ce:

     ku yi sahur haƙiƙa, akwai albarka a cikin yin sahur.

     [Bukhari da Muslim].

    2• Gaggauta yin buɗa baki da jinkirta sahur,

    Saboda faɗin Annabi {s.a.w} ya ce:

    Mutane ba za su gushe suna cikin alkhairi ba, muddin suna gaggauta buɗa baki kuma suna jinkirta sahur.

     [Bukhari da Muslim].

    3• Yin buɗa baki da dabino:

     Manzon ALLAH {s.a.w} ya ce:

    Idan ɗayanku zai yi buɗa baki ya yi buɗa baki da dabino, idan bai samu dabino ba, ya yi da ruwa, don tsarki ne ko tsarkakakke ne.

    [Abu Dawud da Tirmizi].

    4• Addu’a ya yin buɗa baki:

    عَنْ عَبْدِ اللهِ ابْنِ عُمَرُو بْنِ الْعَاص: أَنَّ النَّبِيِّ صَلَّى اللهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ قَالَ: "إِنَّ لِلصَّائِمِ عِنْدَ فِطْرِهِ دَعَوَةٌ مَا تُرَد." (رواه ابن ماجه).

     Abdullahi Ɗan Amru Ɗan As (R.A) ya ce:

     Manzon ALLAH {s.a.w} ya ce:

    Haƙiƙa, mai Azumi idan ya yi addua lokacin buɗa baki ba a mayar da addu’arsa (ana amsawa).

    [ Ibn Majah ne ya rawaito]

    Annabi {s.a.w} ya kasance idan zai yi buɗa baki yana cewa:

    Ya UBANGIJI dominka mukayi Azumi, kuma da arzikinka muke buɗa baki, ka karɓa daga garemu, lallai kai mai jine masani.

    [Abu Dawuda ne ya rawaito].

     Dama wasu addu'o'in da dama.

    5• Asuwaki: Anso ga mai Azumi ya yi asuwaki lokacin azuminsa.

    Saboda Manzon ALLAH {s.a.w} ya kasance yana yin asuwaki lokacin da yake Azumi.

    Haka nan yana daga ladubban Azumi a nisanci shaidar zur, ƙarya, giba, rad'ɗa, rigingimu, da dai sauran ayyukan saɓo.

    ALLAH shi ne mafi sani.

    ************************************** 

    Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

    Question and Answers in Islam

    No comments:

    Post a Comment

    ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.

    HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.