Shin mace za ta iya yin limanci?

    Wannan É—aya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Æ˜ur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waÉ—anda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta Æ™arin fatawowi.

    Amsa

    Na'am ya halatta mace ta yi wa '‘yan uwanta mata limanci.

    Nana A'isha da Ummu Salama (R.A) sun yiwa wasu mata limanci,

    Nawawi ya ce Baihaki ya rawaito wannan hadisi a Sunan nasa, haka kuma Shafi'i a

    Musnad É—insa da sanadi mai kyau, Almajmu'u (4/187).

     Haka kuma an rawaito cewa Annabi {s.a.w.} ya sanyawa Ummu-waraka (R.A) ladani, sannan ya umarceta da ta yiwa matan gidansu limanci, kamar yadda Abu-dawud ya rawaito a hadisi mai lamba ta: 491, kuma Albani ya kyautata shi.

    Saboda haka dalilan da suka gabata sun isa hujja kan halaccin mace na iya yiwa matan unguwarsu limanci, idan dai ta zama tasan hukunce-hukuncen sallah.

    Annabi {s.aw} yana cewa:

    Wanda ya fi iya karatun Alƙur'ani shi ne zaiyi limanci.

    [Muslim 1078].

    Sannan idan mace zatayi limanci wa mata '‘yan uwanta za ta tsaya a

    tsakiyarsu ne, bazata tafi gaba ta tsaya ba, kamar yadda liman namiji yake yiwa maza ba, in kuma su biyu ne, to sai É—ayar ta tsaya a damar wacce take limancin.

    ALLAH shi ne mafi sani.

    ALLAH ka gafarta mana zunubanmu baki É—ayanmu Ameen.

    Question and Answers in Islam

    No comments:

    Post a Comment

    ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.

    HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.