Addu'ar Buɗe Sallah (Du'a'ul Istiftahi)

    𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

    Assalamu alaikum, yayana ina godiya mara adadi, dan Allah ina so a dan kara min bayani a kan addu'o'in da ake yi kafin a ta da sallah.

    𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

    Wa'alaikumus salám, Sahabbai da dama sun ruwaito cewa Annabi ya kasance yana buɗe sallah da addu'o'i da dama da suka haɗa da:

    1. Abu Hurairata Allah ya ƙara masa yarda ya ce: Manzon Allah ya kasance yana yin shiru a tsakanin kabbarar harama da karatu na ɗan lokaci, sai na ce ya Manzon Allah Mahifina da Mahaifiyata fansa ne a gare ka, yin shiru ɗin da kake yi a tsakanin kabbara da karatu mene kake faɗi? Sai Manzon Allah ya ce: Ina cewa ne:

    "اللَّهُمَّ بَاعِدْ بَيْنِي وَبَيْنَ خَطَايَايَ ، كَمَا بَاعَدْتَ بَيْنَ المَشْرِقِ وَالمَغْرِبِ ، اللَّهُمَّ نَقِّنِي مِنَ الخَطَايَا ، كَمَا يُنَقَّى الثَّوْبُ الأَبْيَضُ مِنَ الدَّنَسِ ، اللَّهُمَّ اغْسِلْ خَطَايَايَ بِالْمَاءِ ، وَالثَّلْجِ ، وَالبَرَدِ".

    Bukhariy (744), Muslim (598).

    2. Nana A'isha Allah ya ƙara mata yarda ta ruwaito cewa Manzon Allah ya kasance idan zai buɗe sallah yana cewa:

    "سُبْحَانَكَ اللَّهُمَّ وَبِحَمْدِكَ ، وَتَبَارَكَ اسْمُكَ وَتَعَالَى جَدُّكَ ، وَلَا إِلَهَ غَيْرَكَ".

    Abu Dáwud (776), Attirmizhiy (243).

    3. Daga Aliyu Allah ya ƙara masa yarda ya ce: Ya kasance Manzon Allah idan ya miƙe zai yi sallah yana cewa:

    "وَجَّهْتُ وَجْهِيَ لِلَّذِي فَطَرَ السَّمَاوَاتِ وَالْأَرْضَ حَنِيفًا ، وَمَا أَنَا مِنَ الْمُشْرِكِينَ ، إِنَّ صَلَاتِي ، وَنُسُكِي ، وَمَحْيَايَ ، وَمَمَاتِي لِلَّهِ رَبِّ الْعَالَمِينَ ، لَا شَرِيكَ لَهُ ، وَبِذَلِكَ أُمِرْتُ وَأَنَا مِنَ الْمُسْلِمِينَ ، اللهُمَّ أَنْتَ الْمَلِكُ لَا إِلَهَ إِلَّا أَنْتَ أَنْتَ رَبِّي ، وَأَنَا عَبْدُكَ ، ظَلَمْتُ نَفْسِي ، وَاعْتَرَفْتُ بِذَنْبِي، فَاغْفِرْ لِي ذُنُوبِي جَمِيعًا ، إِنَّهُ لَا يَغْفِرُ الذُّنُوبَ إِلَّا أَنْتَ ، وَاهْدِنِي لِأَحْسَنِ الْأَخْلَاقِ لَا يَهْدِي لِأَحْسَنِهَا إِلَّا أَنْتَ ، وَاصْرِفْ عَنِّي سَيِّئَهَا لَا يَصْرِفُ عَنِّي سَيِّئَهَا إِلَّا أَنْتَ ، لَبَّيْكَ وَسَعْدَيْكَ وَالْخَيْرُ كُلُّهُ فِي يَدَيْكَ ، وَالشَّرُّ لَيْسَ إِلَيْكَ ، أَنَا بِكَ وَإِلَيْكَ ، تَبَارَكْتَ وَتَعَالَيْتَ ، أَسْتَغْفِرُكَ وَأَتُوبُ إِلَيْكَ".

    Muslim (771), Annasá'iy (897).

    Asshaikh Abdul'aziz bn Baaz ya ce: "Wannan addu'ar ta uku Annabi ya kasance yana karanta ta ne a sallar nafila ta dare, amma a sallar farillah, abin da ya fi shi ne karanta waccan addu'ar ta farko ko ta biyu, wannan shi ne abin da aka kiyaye daga gare shi  a sallar farillah, amma buɗe sallah da addu'a mai tsawo ya kasance yana yin ta ne a sallar tahajjud".

    Duba Fataawá Nurun Alad Darb (8/182).

    Baya ga waɗannan akwai wasu addu'o'in da dama da Manzon Allah yakan buɗe sallarsa da su da ba zai yiwu a kawo su duka a nan ba.

    Allah S.W.T ne mafi sani.

    Jamilu Ibrahim Sarki, Zaria.

    𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

    https://chat.whatsapp.com/GcU1I5wjOB18K4PA6eURƘƘ

    𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

    Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

    𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

    https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi

    ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

    **************************

    Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

    Question and Answers in Islam

    No comments:

    Post a Comment

    ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.

    HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.