Assalamu alaikum. Shin Ya Halatta Na Ba Wa Iyaye Na Zakkar Fidda Kai?

     𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

    Assalamu alaikum. Shin Ya Halatta Na Ba Wa Iyaye Na Zakkar Fidda Kai?

    𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

    وعليكم السلام ورحمة الله.

    ﺍﻟﺤﻤﺪ ﻟﻠﻪ ﺭﺏ ﺍﻟﻌﺎﻟﻤﻴﻦ ، ﻭﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻰ ﺳﻴﺪﻧﺎ ﻣﺤﻤﺪ ﻭﻋﻠﻰ ﺁﻟﻪ ﻭﺻﺤﺒﻪ ﺃﺟﻤﻌﻴﻦ، ﻭﺑﺎﻟﻠﻪ ﺍﻟﺘﻮﻓﻴﻖ،

    Malamai sun yi ittifaaƙi a kan cewa bai halatta ba mutum ya ba da zakkatul mafrud (Kamar zakkar fidda kai) ga waɗanda nauyinsu ya rataya a wuyansa, kamar Iyaye da 'ya'ya.

    An fada a cikin Al-Mudawwanah (1/344): Toh zakkar dukiya ta fa, su waye bai halatta Na bawa ba abisa ra'ayin imam malik??.

    Yace; Malik ya ce: Karka bada ita ga duk wani ɗan'uwanka wanda nauyinsa yake akanka.

    Al-Shaafa’i yace a cikin Al-Umm (2/87): Bazai bada (Zakkar dukiyarsa) ga Mahaifinsa ba ko Mahaifiyarsa ko Kakansa ko Kakarsa ba.

    Ibn Ƙudaamah (rahimahullah) yace a cikin Al-Mughni (2/509): Babu daya daga cikin Zakkah ta farillah da za a bawa Iyaye komai nisan nasabarsu (ma'ana Kakanni maza da Kakanni mata) ko 'Ya'ya komai Nisan nasabarsu (ma'ana Jikoki).

    Ibn Mundhir (rahimahullah) ya ce: Malamai sun yi ittifaaƙi a kan bai halatta ba abawa iyaye zakkah ba, a yanayi na kasancewar nauyinsu ya rataya a wuyansa. Saboda haka basu zakkah tamkar shi ne ya bawa kansa zakkah da kansa. Basu zakkah kamar Yana nufin su basa bukatar taimakon komai a wajensa ne, kuma babu nauyinsu na dawainiyarsu a wuyansa.

    والله أعلم،

    Ga Masu Buƙatar Shiga Wannan Group Zaku iya bi ta Links ɗin mu...

    𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

    https://chat.whatsapp.com/JLojawdOWYsEOeSHZMNdjf

    𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

    Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

    𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

    https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi

    ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

    **************************

    Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

    Question and Answers in Islam

    No comments:

    Post a Comment

    ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.

    HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.