Babu Bambanci Tsakanin Sallar Namiji Da Ta Mace!

 𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

Assalamu alykum, Idan mata suna jam'in sallah shin limamiyarsu za ta jiyar dasu katarun fatiha da sura (awajen bayyanawa)? za ta bayyana kabbarori yadda za ta jiyar da su? kuma zasu haɗa ƙafafuwansu a sahu kamar yadda maza suke?

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

Wa'alaikum assalam, Babu bambanci tsakanin sallar mace da ta namiji a zance mafi inganci, saboda babu nassoshi yankakku waɗanda suka bambanta, don haka in mace ta yiwa mata limanci za ta jiyar da su karatu kamar yadda namiji yake jiyar da mamunsa maza, za su haɗa sawu saboda zukatansu kar su saba.

Idan mace ta limanci 'yan'uwanta mata za ta tsaya ne a tsakiyarsu, in har ya zama akwai maza a kusa waɗanda ba muharramai ba, macen za ta iya yin kasa da muryarta saboda kada su fitinu da ita.

Allah ne mafi sani.

Amsawa🏻

DR. JAMILU YUSUF ZAREWA

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

https://chat.whatsapp.com/LMfHgWHKrUG9c16dKf9ZBH

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam

Post a Comment

0 Comments