Bayan Ta Haihu, Ta Yi Wajen Wata Biyu Jinin Al'ada Bai Dawo Ba

     𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

    Assalamu Alaikum Warahmatallahi Wabarkatahu

    Wata matace, ta haihu ne to ta yi wajan 2 month period nata baidawo ba sai randa aka dau azumi ta ga wani abu mai yauki kaman majina amman yana hadeda jini sai dai jini ba ja sosai bane kuma baya karni sanna kuma yayita zuwa ne kaman majina har tswon kwana uku to yanzu wannan kam za ta biya azumin ne sanna kuma intazo yin wanka wani irin niyya zatayi??

    𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

    To wannan tambayar akwai wani abu a cikinta, abun kuwa shi ne akwai buƙatar musani shin sadda ta haihun ta ga jini kokuwa bata ganiba?? Idan ta ga jini sai jinin ya dauke shi ne bayan daukewarshin har watanni biyu bata ga al'adarta ba, sai bayan watanni biyun ta ga wannan kalarda tace tagani?? To idan haka take nufi, to inhar tana iya gane kalar jinin hailarta saita duba tagani, inhar wannan ruwan shi ne irin jinin hailarda tasaba gani dama aduk lokacin hailar, to shikenan wannan din datagani yanzu to hailace dan haka bayan sallah za ta rama azumin wayannan kwanakin sannan kuma niyyar wankan haila za ta yi.

    Inkuwa sanda ta haihun kwata kwata bata ga jiniba sai wannan wanda tace taganshi a bayan watannin biyun to shima dai hukuncin iri dayane da bayaninda mukayi asama

    Amma dan wannan ruwan bashi ne irin jinin hailarda tasabayi ba, to anan za ta bashi hukuncin damu fasadinne wato jinin ciwo, kenan azuminta na wayannan kwanakin sunyi, sannan kuma babu wankanda zatayi saidai wanka na tsafta da jin daɗi

    Inkuma wannan kalar da ta gani ya zo matane kafin ta cika kwanaki 40 ko 60 da haihuwa shi ne ta ga wannan kalar ruwan to anan kuma jinin haihuwane dan haka ba ta da azumin wayannan kwanakin, sannan kuma wankan da zatayi shi ne na yankewar jinin haihuwa

    Allah ya sa mudace

    𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

    https://chat.whatsapp.com/Du5LNx31U9hDi6RƘbbrzgW

    𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

    Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

    𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

    https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi

    ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

    **************************

    Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

    Question and Answers in Islam

    No comments:

    Post a Comment

    ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.

    HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.