Macen Da Al'adarta Ta Zo Mata A Goman Qarshe Ya Za Ta Yi Ta Rabauta Da Lailatul Qadari?

    Duk wacce ALLAH yasa Al'adarta ta zo mata a wannan goman ƙarshe, haƙika an haramta mata shiga masallaci don yin sallah, kuma ko da ita kaɗaice sallah da Azumi ba za ta yisu ba.

     Amma saboda tanason ta ribaci kwana goman da wata ibadah, domin haɗuwa da wannan daren, to sai ta farka a dare, sai ta ɗauki Alƙur'ani ta karanta abin da ya sauwaƙa, suratul fatiha ce ko wata surar, idan taso ta yi ta maimaita sura ɗaya, idan taso kuma ta karanta wasu.

     Bayan ta gama sai ta yi istigfar gwargwadon iko, ta yi salati ga Annabi {s.a.w},

     Sannan ta ɗaga hannun ta sama ta roƙi ALLAH dukkan buƙatarta, in sha ALLAH za ta rabauta da wannan dare, indai ta raya dararen ko da ta hanyar karanta Alkur'ani ne.

    ALLAH ka azurtamu da wannan dare mai albarka.

    ALLAH ka gafarta mana zunubanmu baki ɗayanmu Ameen.

    ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

    **************************

    Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

    Question and Answers in Islam

    No comments:

    Post a Comment

    ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.

    HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.