Shin Wajibi ne Uba Ya Fitar wa Da 'Ya'yansa Zakkar Fidda Kai?

     𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

    Shin Wajibi ne Uba Ya Fitar wa Da 'Ya'yansa Zakkar Fidda Kai?

    𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

    Zakkar fiddakai tana cikin ibadoji farillai wanda mutum zai bayar da kansa ko ta hanyar wakilinsa.

    Saboda haka ba wajibi bane ya fitarwa da 'ya'yansa zakkar fidda-kai idan sun kasance baligaine kuma masu hankali, mawadatane ko talakawa, amma idan ba balagaggu bane, idan suna da dukiya to zakkar fidda kansu za a fitar daka dukiyarsu, idan basu da dukiya zakkar fidda kansu tana kan mahaifinsu ko da suna karkashin kulawar uwarsu ne datake aure a wani wajan.

    Imamun Nawawi rahimahullah ya ce: Idan yaro bashi da dukiya to zakkar fidda kansa tana kan babansa, wajibi ne babansa ya yi masa ita a ijma'in malamai, Abu hanifa da ishaƙ, da Abussauri suntafi a kan haka.

     Duba Almajmu'u (6/108).

    Ya sake cewa: Idan yaro yanada wadata ciyarwarsa da zakkar fidda kansa suna cikin dukiyarsa bata kan babansa ko kakansa, Abu hanifa, da Ahmad da muhammad da Ishaƙ, a kan haka suka tafi, ibnu munzir ya ruwaito daka wasu malamai, cewa: zakkar fidda kansa tana kan babansa, idan yafitar daka dukiyar yaro ya yi sabo, sannan zai mayar masa dukiyarsa.

    Idan ka tabbatar da wannan, babu ban-banci wajan wajabcin zakkar fiddakan kananun yara a kan mahaifansu, Suna karkashin kulawar mahaifiyarsu ko suna karkashin kulawar waninta, domin ciyar da su wajibi ne akansa idan basu da dukiya a ijma'in malamai, hakama zakkar fidda kai.

    Ibnu munzir rahimahullah ya ce: Duk waɗanda muka haddace cikin ma'abota ilmi sun yi ijma'i ciyarwar yara kananan dabasu da dukiya tanakan mahaifinsu,

    Almugni(8/169).

    WALLAHU A'ALAM.

    Ga Masu Buƙatar Shiga Wannan Group Zaku iya bi ta Links ɗin mu...

    𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

    https://chat.whatsapp.com/GcU1I5wjOB18K4PA6eURƘƘ

    𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

    Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

    𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

    https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi

    ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

    **************************

    Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

    Question and Answers in Islam

    No comments:

    Post a Comment

    ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.

    HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.