Baubawan Burmi

    Yakasai, S. A. & Sani, A-U. (2021). Diwanin WaÆ™oÆ™in Aminu Ladan Abubakar (ALA)Kaduna: Amal Printing & Publishing Nigerian LTD. ISBN: 978-978-57624-9-0.

    Amshi:

    Baubawan birni kasassaɓar mu ce kan zaɓen jagora iye iye.

     

    Allah malikal mulki tutal mulki mantasha’u a kan mulki,

    Allah mun yi zaman dirshan tamkar fitila a lokon alkuki,

    Sai a ka ɗa mu a rau rayar Allah na mu na buƙatar jagora.

     

    Sallu alaika Rasulullah É—an Amina ma fi tsarkin jagora,

    Ahlihi har asahaba masu biya biyar É—afa gun jagora,

    Mai alfarma da agala Ahmadu hamidun fiyayyen jagora.

     

    Allah ka san kukana ka san hujjar zubar da hawayena,

    Bauta ce ta canza ta É—auko salo da tsari mummuna,

    Mun bar mulkin mallaka kama karya a yau shi muka É—ora.

     

    Dole in koka da tsiwa,

    Dubi ƙasar nan Arewa,

    Ba ilimi talakawa,

    Ba mu da aikin taɓawa,

    Mun zama jujin zubawa,

    Tarkacen tarkatawa.

      

    Dangi a duba min hanya da can da muna a mulkin mallaka,

    Wahala dai aka ba bawa amma duk tsiya abinci a ba ka,

    Yanzu ko gadonmu talauci ai kuÉ—ar sa ta fi dukan ka da gora.

     

     

     

     

    Talauci shi muka gado jahilci ko ya zamanto rigarmu,

    Ba mu da ikon yin mulki balle mu ciro masharin kukan mu,

    Mun É—ore da tumasanci mabarata muke a hannun jagora.

     

    Dangi a waiwaya a duba makarantunmu daban ne da na ‘ya’yansu,

    La’akari da abincinsu kama har zuwa ruwan da suke sha su,

    Kai duba da makwancinsu daga nan za ka gane mungun jagora.

     

    Sannan ba sa alkunya daga an doka tamburan nan na siyasa,

    Kunya ba tsoron Allah su yi oda ta atamfar nan sosa,

    Su mammanna gumakansu su rarraba mu É—auke su mu É—ora.

     

    A zokoto da bawa ƙarar kuka da tsuwa,

    Mun shagaltu da yunwa,

    Mun dishe da ƙishirwa,

    Mun makance da sowa,

    Allah kai ke sauyawa.

    Suke tarkata yaranmu da makamai suna ta saran junansu,

    Inda alamar adalci to me zai hana su cakuÉ—a ‘ya’yansu,

    Kayan maye suka ba su su hau gidan mutum su faÉ—a shi da sara.

     

    KuÉ—in abinci ake ba ku an maishe ku sai ka ce dabbar kiwo,

    KuÉ—i a dumtse su a watsa ku bi kuna ta wawaso har ku ji ciwo,

    Ungulu za dai fa a koma gidanki dai na tsamiya daina gadara.

     

    Allah wanga kashin mulki ya yi kama guda da kashin dankali,

    Na sama ya danne na ƙasa idan ya so numfashi babu dalili,

    Jin daÉ—in su kawunansu alfarmarsu iyalansu na kibira.

     

    Allah kai ka ban iko in ƙi abin gudu da fatar bakina,

    Allah kai ka ban hikima in yi ragargaza da harshen bakina,

    In faÉ—akar gun al’umma don su Æ™yamata ga mulki na gadara.

     

    Dangi Aminuddeen ALA na Tudun Murtala na kwanar yan Ghana,

    Shugaban yan shangwago mai kulakuci da ƙawa dangina,

    Shi ne ke muku adabo sai wataran idan muna da yawan kwana.  

    Daga Diwanin Waƙoƙin Aminu Ladan Abubakar (ALA)

    No comments:

    Post a Comment

    ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.

    HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.