Haddin Wanda Ya Auri Matar Babansa Ko 'Yarsa

    Shari'ar musulunci ta halatta jini da dukiyar wanda ya auri matar babansa ko '‘yarsa, saboda ya halatta abinda ALLAH ya haramta.

     Daga Barra'u (R.A) Ya ce:

    Na gamu da Ammina yana ɗauke da tuta tare dashi, sai nace ina ka nufa?

    Sai ya ce:

     Manzon ALLAH {s.a.w} ne ya turani izuwa wani mutum daya auri matar mahaifinsa, kuma ya umarceni da na sare kansa na kuma kwaso dukiyarsa.

     Saboda haka halatta abinda ALLAH ya haramta kafirci ne, ridda ne, barin musulunci ne, duk wanda ya halatta abinda ALLAH ya haramta haƙiƙa ya yi ridda, ya zama kafiri.

     Don haka auren matar mahaifinka ko da bayan mutuwarsa ne, ko mutum ya auri '‘yarsa yana sane bawai a rashin sani ba, to wannan kafirci ne, hukuncin kisa yahau kansa.

    ALLAH ka bamu ikon aiki da abinda muka karanta.

    ALLAH ka gafarta mana zunubanmu baki ɗayanmu Ameen.

    ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

    **************************

    Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

    Question and Answers in Islam

    No comments:

    Post a Comment

    ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.

    HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.