Sarautar Ubangiji

     1-

    Da sunan Ubangiji,

    Da dake bamu agaji,

    Ya yi komai aji-aji,

    Da tsuntsu da fiffike.

    2-

    Suradhal Lazi ya ke,

    Da an bi Shi an fake,

    Halittarmu Shi yake,

    A koman daban Ya ke.

     

    3-

    Yana ci da tsurruka,

    Da ƙwari a tsaunika,

    Da yai kum! da an haka,

    A bauta ga shi mu ke.

     

    4-

    Bai haifa ba Ƙadiran,

    Muridan mubasshiran,

    Gwani anta ƙalikhan,

    Fiyayye da Kai na ke.

     

    5-

    Shi ke bamu lafiya,

    Idan babu tun jiya,

    Shi ke kare duniya,

    A koma ina ta ke.

     

    6-

    Shi ke kai mutum sama,

    Ya koro shi ya  gama,

    Ba a faÉ—ar ka ka gama,

    Ka san Shi daban Ya ke.

     

    7-

    Kuna zaune lafiya,

    Ya watso hajijiya,

    Take zaga Nahiya,

    Gidajen zuba su ke.

     

    8-

    Da lotonka ya wuce,

    A rannan da ka mace,

    Za ka zama kamar ice,

    In sharholiya ka ke.

     

    9-

    Sarauta ga Shi ta ke,

    In ya baka ka sake,

    Bala'an a nan su ke,

    Don Ya baka ka sake.

     

    10-

    Wanda Ya ƙagi duniya,

    China ƙasar ltaliya,

    Ghana da Y'an Nijeriya,

    Dukka a ƙarƙashi mu ke?

     

    11-

    Shi Allahu Ya sani,

    Don baya biÉ—ar tuni,

    Komai namu Ya sani,

    Ka bar wai ina Ya ke?

     

    12-

    Ka kai kanka lahira,

    Ka zo nan ka sha jira,

    Da kwananka yai kira,

    Da ka san ina Ya ke!.

     

    13-

    Mata ban da É—an cikin,

    Ta dawo ga Maliki,

    A rannan abin cikin,

    Zai fita ko ina take.

     

    14-

    Zai kuma rayu duniya,

    Ya lalleƙa Nahiya,

    Ya je Umma'ahiya,

    Tunaninsa ma ake.

     

    15-

    Ku dudduba dazuka,

    Duwatsu da tsaunuka,

    Halittu a ramuka,

    FaÉ—ar Rabbana su ke.

     

    16-

    Kana kwance ka mutu,

    A na wane ya mutu,

    Su lamin da Saratun,

    Ba su kiran ina ka ke!

     

    17-

    Ka fita fes da sallama,

    Ka dawo kamar rama,

    Kai hatsarin arangama,

    Ba ka sanin ina ka ke?

     

    18-

    Jari Ya baka mai yawa,

    Kullum sui ta hauhawa,

    Randa ya sake waiwaya,

    Baka sanin  ina su ke!

     

    19-

    Da can kun ta'azzara,

    Yanzu ko kun tagayyara,

    Don haka sai ku ankara,

    Yau damarku ya take?

     

    20-

    Allah gani na tsaya,

    Kangala ne na tambaya,

    Zan wa'azi da É—auraya,

    Kan ikonKa ya ka ke.

     

    Marubuci:-

    Abdullahi Lawan Kangala

     

    Haƙƙin Mallaka:

    Phone:- +2348033815276

    KANGALA GLOBAL AWARENESS VIA MEDIA

    No comments:

    Post a Comment

    ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.

    HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.