Waƙar Keke Ta (Dr) Aliyu Namangi Zariya

    Muna shukura ga Rabbal alamina

    Da alherin da yai mana ba kaɗan ba.


    Muna murna da mulkin Ingilishi

    Zuwan da sukai ƙasarmu ba tai tsiya ba.


    Zama zamaninsu ne aka zo da faifa

    Kuɗi ba masu nauyaya aljihu ba.


    Daɗa zarafinsu ne aka zo da jirgi

    Ka je Makka ba da tashin hankali ba.


    Sa'annan ga su Babur, ga su Mota

    Da farko a da can ba mu san da su ba.


    Izan tafiya ta faru ka nemi mota

    Izan jirgi ba kui daidai da shi ba.


    Izan kuwa babu Jirgi babu mota

    Ka je da ƙafarsa ba keken tsiya ba.


    Banni da Basukar ho, ɗan jidali

    shaƙiyyi ba abin babba ya hau ba.


    A Ɗanmahawayi nih hau sai ya bar ni

    Tudun-Yakaji ban kawo gari ba.


    Ya bar ni da jin jiki da zama a turba

    Da ɗai ko juma'a ba a je da ni ba.


    Kuɗi tirmis, na ba shi sule-da-sisi

    keke bai mani rangwame ko da ɗari ba.


    Na ce masa "Basukur riƙa sawwaƙewa"

    Ya ce "Malam hala ba ka sanni ne ba".


    Ina da tsiya biyar farkonsu fanca

    Na kau buga bindiga ba mai wuta ba.


    In babbake zuciya, in tafi da sawu

    Cikin daji kamar ba a je da ni ba.


    Muna tafiya kuma na fizge kaina

    Mu faɗa kwazazzabo ni ban kula ba.


    Ina da ciki ana ce mai kurumbo

    Karambanin hawa ba ka saya ba.


    Hanjina kaca mai kama riga

    In fizgo mai hawa ni ban kula ba.


    Tsiya na can mu je kan kadarko

    Madaidaici in ce ba za mu hau ba.


    In hau bisa kafaɗar bari na zauna

    Kamar mahayin daɗai bai hauni shi ba.


    Sukai ka'ida da Sale a kan kadarko

    Sai yace "Haba Sale ba zan yadda kai ba.


    Daɗai suka wantsala hakan kan ya ƙwace

    Ashe ba Sale ne a cikin ruwa ba?


    Ya bi shi ya bangaje ya buge yana ce

    A zo a gani idan ban yada kai ba.


    Malam Sale sai da ya tuɓe riga

    Ya sa ka ga Sale har bai sha ruwa ba.


    Ya tashi ya hau tudu keke ya bi shi

    Da rigar Sale keke bai sako ba.


    Su malam Sanda duk suka tarma keke

    Da ban magana ya ce ba zai sako ba.


    Ya ma rantse da jirgi har da mota

    Ba za shi sako in ba a sa wuƙa ba.


    Malam Sanda wai sun shirya da keke

    Wai yana ƙaunarsa ba domin tsiya ba.


    Ya ce haba malami kamarka

    Ba zan iya yadda babban malami ba.


    Izan dai za ka hauni ka tara riga

    Da wando ba ka hau ni hawan isa ba.


    Ya tashi hawa bai tattara ba

    Ya fizgo malamin ba a jinjima ba.


    Ya yasai nan da nan a tsakar gidansa

    Cikin matansa tun ba a kai daɓe ba.


    Yace Bari nai kure yashe ka malam

    Dama ban kai ka bakin kasuwa ba.


    Ba na son na yada mutum na kirki

    Izan ba inda za ai dariya ba.


    Da motsa ƙararrawarka da kama burki

    Ba za su hana ni in jefar da kai ba.


    Ya ce masa ba na ƙara hawanka keke

    Ya ce masa ko adankiya ban kula ba.


    Hawan da rashin hawan a gare ni ɗai ne

    Ban ga abin da zai cutar dani ba.


    Kamar tafiya ta sauri ko ta fizge

    Ba ka je inda ka so nan da nan ba.


    Izan ka zo ka hau ni ka ba ni iska

    Na sha, ba inda ba zan je da kai ba.


    Ashe ba mai hawa keke ya more

    Izan ba wanda ya iya zanzaro ba.

    Ɗaukowar:

    Abbas Musa Jega
    abbasmusajega750@gmail.com.
    Ɗalibi A Sashen Harsunan Nijeriya Jami'ar Usmanu Ɗanfodiyo Sakkwato.

    No comments:

    Post a Comment

    ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.

    HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.