3.1.4 Ta Gidan Malam Audu - Daga Littafin WAƘOƘIN HAUSA NA GARGAJIYA (Page - 99)

    Citation: Gobir, Y.A. & Sani, A-U. (2021). Waƙoƙin Hausa Na Gargajiya. Kaduna: Amal Printing & Publishing Nigerian LTD. ISBN: 978-978-59094-0-01.

    3.1.4 Ta Gidan Malam Audu

    Wannan waƙa ana yin ta ne a cikin lugude. Ta kasance tamkar gaisuwa ce tsakanin masu daka, inda idan ɗaya ta yi gaisuwa sai guda kuma ta amsa mata. Ga yadda abin yake kasancewa:

    Ke ta gidan, ke ta gidan,

    Ke ta gidan Mallam Audu.

     

    Uwar gidan Malam Audu,

    Sha lelen Mallam Audu.

     

    Ina yininki?

    Binta ina yininki?

     

    Gaisuwa da aminci,

    Yarda ta fi aminci.

     

    Hausa tana gaishe ki,

    Kin kwana lafiya?

    Kin tashi lafiya.

     

    Wadda ake lugude da ita za ta ba da amsa kamar haka:

    Ke ma kin tashi lafiya?

    Ke ma ina gaishe ki,

    Kin yini lafiya?

    WAƘOƘIN HAUSA NA GARGAJIYA

    No comments:

    Post a Comment

    ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.

    HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.