3.2.2 Bawan Allah - Daga Littafin WAƘOƘIN HAUSA NA GARGAJIYA (Page - 101)

    Citation: Gobir, Y.A. & Sani, A-U. (2021). Waƙoƙin Hausa Na Gargajiya. Kaduna: Amal Printing & Publishing Nigerian LTD. ISBN: 978-978-59094-0-01.

    3.2.2 Bawan Allah 

    Wannan ma waƙa ce ta ɗaɓe. Tana ɗauke ne da kalaman tausaya wa talaka, inda ake nuna ba shi da ƙarfin faɗa a ji ko kare kansa daga cutarwar azzalumai. Ga yadda waƙar take:

    Bawan Allah,

    Talakka bawan Allah.

     

    Ba shi da baki,

    Balle shi furta kalami.

     

    Ba shi ƙafafu,

    Balle shi tashi shi tsere.

     

    Bawan Allah,

    Talakka bawan Allah.

    WAƘOƘIN HAUSA NA GARGAJIYA

    No comments:

    Post a Comment

    ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.

    HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.