Gamda'are

    Zumu /Ɗan Uwa na ji ni. Ko a wannan Waƙar wanda aka ce ma Sarkin Ƙaya Tambari Gamda'aren shi watau Sarkin Rafin Dosara (Gamda'aren Sarkin Rwahi) ɗan uwan shi ne na jini domin duk wanda ke Sarautar Dosara ya na iya zamowa Sarkin Ƙayan Maradun. Bayan rasuwar Malam Muhammadu Mu'alliyeɗi ɗan Sarkin Musulmi Muhammadu Bello ɗan Mujaddadi Shehu Usman Ɗanfodio tagammadahullah birahamatihi, Sarkin Ƙayan Maradun na biyu da ya biyo bayan shi ɗan shi ne, Alhaji dake sarauta a Dosara da laƙabin Sarkin Rafi.

    Idan ka saurari Waƙar Makaɗa Alhaji Musa Ɗanƙwairo Maradun ta Sardaunan Sakkwato, Sir Ahmadu Bello GCON KBE mai amshi 'Kada Marake Giwa.. Ya na cewa "Gamda'aren Sarkin Musulmi, na Alƙalin Alƙalai manyan Hausa Uban Janjuna.. /Kaga Sarkin Musulmi Abubakar III ɗan Uwan Sardaunan Sakkwato ne jini domin dukan su daga Zauren Sarkin Musulmi Muhammadu Bello ɗan Mujaddadi Shehu Usman Ɗanfodio suka fito. Sarkin Musulmi Abubakar III ɗan Modibbo Usman ne, Modibbo Usman ɗan Sarkin Musulmi Mu'azu ne, Sarkin Musulmi Mu'azu ɗan Sarkin Musulmi Muhammadu Bello ne, Sarkin Musulmi Muhammadu Bello ɗan Mujaddadi Shehu Usman Ɗanfodio ne. Sardauna Ahmadu Bello ɗan Sarkin Raɓah Ibrahimu ne, Sarkin Raɓah Ibrahimu ɗan Sarkin Yan Shawara(Zartu Yan Shawara) /Sarkin Raɓah /Sarkin Musulmi Abubakar II (Mai Raɓah) ne, Sarkin Musulmi Abubakar Mai Raɓah ɗan Sarkin Musulmi Muhammadu Bello ne, Sarkin Musulmi Muhammadu Bello ɗan Mujaddadi Shehu Usman Ɗanfodio ne.

    Makaɗa Ibrahim Narambaɗa Tubali ya na cewa "Mai Gusau raba kaya, ba a kaima ka wargi, Mai rabo da yawa gamda'aren Sarkin Gobir" a cikin Waƙar shi ta Marigayi Mai Girma Uban Ƙasar / Hakimin Gundumar Gusau, Marigayi Sarkin Kudun Gusau, Alhaji Sulaiman Ibrahim Isa. Gamda'aren Sarkin Gobir na Isa Amadu I ya ke nufi. Da Sarkin Gobir na Isa Amadu I da Sarkin Kudun Gusau, Alhaji Sulaiman Ibrahim Isa daga gida suka fito Zuriyar Sarkin Musulmi Aliyu ɗan Sarkin Musulmi Muhammadu Bello ɗan Mujaddadi Shehu Usman Ɗanfodio.

    Daga Taskar

    Malam Ibrahim Muhammad Birnin Magaji
    ÆŠanmadamin Birnin Magaji
    Imel: birninbagaji4040@gmail.com
    Lambar Waya: 08149388452, 08027484815 

    No comments:

    Post a Comment

    ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.

    HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.