Game Da Dame Da Waɗansu 'Yan Dambe

    Na Mai Ango a Birnin Magaji ya fara Dambe ya na ɗan matashin shi a farko farkon 1980s. Ƙauyen su da ake kira Riyoji ya na yamma da garin Birnin Magaji duk da yake suna cikin Masarautar Zurmi ne.

    Riyoji garin Madambata ne da ke da asirin Dambe sosai. Nan aka yi Aikau da Jijji da Issau da Olo da sauran su. Na Mai Ango wanda Ɗanbalade ke kira Ɗan Ango a cikin Waƙar da ya yi mashi ya taso a matsayin ɗan dambe marar fargaba da wayon dambe da kuma neman asiri sosai. Allah ya jiƙan shi.

    Daga Taskar

    Malam Ibrahim Muhammad Birnin Magaji
    Ɗanmadamin Birnin Magaji
    Imel: birninbagaji4040@gmail.com
    Lambar Waya: 08149388452, 08027484815 

    No comments:

    Post a Comment

    ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.

    HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.