Ilmi (Education) Ta Aliyu Idris

    Ai dole ne mui nazari,

    A batun ilimi ya zarta.

     

    Ga karatu yai tsada,

    Ilmi fa sai mai gata.

     

    Cikin shekara su dad'a,

    Muna ƙangin bauta.

     

    Dama muna ji kullum,

    Kakanu sun mana bita,

     

    Suna fad'in wata rana,

    'Dan talaka zai nisanta.

     

    Ilmi fa zai yo wahala,

    Wahala ta sa su gujeta.

     

    Ga shi 'ya'yan talaka,

    Wasu duk sun gigita.

     

    Da akwai marasa kishi,

    Ilmin ƙasar suka 6ata.

     

    Yau Najeriya ba daraja,

    Ku tsaya kui fuskanta.

     

    'Ya'yan su na can turai,

    Na mu sun bambamta.

     

    Kun ga kenan ba adalci,

    Tun da sun mana rata.

     

    Haka shi ne manufar ku?

    Rayuwarmu kun cuceta.

     

    Hakkinmu ne kuka tauye,

    'Yanci mu kun yi farauta.

     

    Yanzu ba nation builders,

    Ga leaders suna ƙaisata.

     

    (C)Aliyu Idris
    (Sarkin Yaƙin Malumma)
    21/07/2023


    No comments:

    Post a Comment

    ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.

    HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.