Ma'anar Kudu Da Arewa Da Ake Ambata A Wasan Dambe

    Ɓangarorin dambe ne da ake rabawa gida gida. Yandamben arewa galibi sun fito ne daga jihohin Zamfara da Sakkwato da kabi da wani sashe na jihohin Naija da katsina amma haka bai hana a same su inda ake samun kudawa,misali,Nabacirawa da Bala Yaro da Sani yaron Mamman da Hussaini Ɗankwalle na Toronkawa wadanda yan jihar Kano ne da Kaduna da Katsina. Kurdawa kuma, ya ƙunshi yandamben da suka fito daga yankunan Kano har zuwa Maiduguri. Amma yanzu Arewa ko Jamus ta rabu biyu. Akwai arewatawa akwai gurumaɗa daga jihar kabi. Har wa yau,akwai yandamben da ake kira Daurawa, wanda mutanen Daura ne.

    Daga:
    Zauren Makaɗa Da Mawaƙa

    No comments:

    Post a Comment

    ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.

    HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.