Meye Mafita Ga Mace In Ba Ta Samun Zuwan Kai Lokacin Saduwa?

    𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

    Assalmu Alaikum, don malam a amsamin wannan tanbayar Matsalata ita ce idan na kwanta da mijina bana gamsuwa, meye mafita?

    𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

    Wa'alaikumussalam. To yar uwa akwai banbanci tsakanin inzali na mace Dana namiji domin yanzu matsalar da wasu mata ke ciki shi ne basajin lokacinda suke inzali kamar yanda namiji ke sani kuma bisa binciken masana Abu ukune kan gaba wajen faruwan wannan matsalar.

    1. akwai infection (ciwon sanyi) Wanda yake hana mace sanin lokacinda take inzali domin maniyinta zai tsinke ya zama kamar ruwa zai rinka fitowa kaɗan kaɗan wata tana jin daɗi lokacin fitarsa wata kuma kwata kwata babu abin da takeji na daɗi amma mijinta zai iya jin daɗin shima kafin ciwon yayi yawa saboda irin masu wannan matsalar koda maganin ni'ima sukayi babu wani canji to a hankali saishima mijin yadena jin daɗinta kuma sauda dama abin da ke kawo wannan matsalar shi ne wasa da farji lokacin mace tana budurwa ko kuma saka abin da bashida Inganci to abin da za kiyi shi ne kirinka tsarkida ruwan dumi da magarya aciki kuma kisamu garin hulba da gishiri kaɗan ki zuba a ruwan dumi kina zama shima lalle za ki iya dafa ganyen danyensa dandano ba Zuma kinasha sannan me irin wannan matsalar zata iya amfani da miski na matsi wato miskul dahara tana matsi dashi.

    2. Na biyu akwai rashin gamsuwa da miji shima yana hana mace inzali domin wasu matan ana dadewa kafin suyi zuwan kai to idan ya zama mijin bashida juriyar dadewa mace sai taji kamar zaizo amma ba dama ko kuma kankantar gaban namjji baya shiga gaban mace yanda ya kamata to babu damar tayi inzali to wannan matsalar daga wajen mijinne suna iya wasanni sosai har saita kusa yin inzalin kafin afara saduwa.

    3. akwai rashin sha'awa mace Wanda batajin sha'awar namiji komai dadewa ana saduwa da ita bazatayi inzaliba irin wannan gaskiya ta dage dashan magungunan kara sha'awa tare da ni'ima.

    Allah ta'ala yasa mudace.

    Zauren Fatawowi Bisa Alkur'ani Da Sunnah, ta fahimtar magabatan ƙwarai.

    𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

    https://chat.whatsapp.com/JoWs3feDfdyGE9yBsa1RSC

    𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

    Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

    𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

    https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi

    ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

    **************************

    Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

    Questions and Answers

    No comments:

    Post a Comment

    ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.

    HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.