Zan Iya Fita Ba Tare Da Izinin Mijina Ba, Idan Iyayensa Suka Ba Ni Izini?

    𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

    Idan mace suka samu saɓani da mijinta saita gaishe shi yaki amsawa, ta tambayeshi zata gaida mahaifiyarta nan ma yaki amsa mata, shin zata iya tambayar iyayensa insun ba ta izini saitaje, hakan yayi dai-dai acikin musulunci?

    𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

    الحمد لله

    Malamai sunyi ittifaƙi a kan haramcin fitar mace ba tare da lalura ba, ko wajabcin shari'a, ba tare da izinin mijinta ba, suna kirga matan dasuke aikata hakan cikin kangararrun mutane, baudaddu.

    Ya zo a cikin Mausu'ah fiƙhiyyah (19/107)

    Asali shi ne mata an Umarcesune dasu lazimci gidajensu, kuma an hanasu fita, bai halatta ga mace tafita ba saida izinin mijinta.

    Ibnu hajar haitami ya ce: Kod a mace ta takura wajan ziyartar mahaifiyarta za ta fita da izinin mijinta ba tare da kwalliya ba.

    Ibnu hajar asƙalani yaruwaito daka nawawi wajan ta'aliƙin hadisin (Idan matayenku suka nemi izininku zuwa masallaci da daddare kuyi musu izini) ya ce: yakafa hujja dashi cewa mace bazata fita daka gidan mijintaba saida izininsa, saboda an fuskantar da izinin ga mazajensu.

    Hakama budurwa bazata fita daka gidaba saida izinin waliyyinta mahaifinta ko ɗan'uwanta wanda dai yake kula da tarbiyyarta, musamman saboda lalacewar zamani dacanjawar al'amura, wajibine ga waliyyinta ya ɗauki wannan nauyin ya kiyaye amanar dake wajansa, tayanda zai haɗu da Allah yaladabtar da ita ya ba ta tarbiyya ya kyautata mata ya ba ta ilmi, Abin da yake tilas awajan budurwa shi ne ta kiyaye kada ta saɓa masa a kan irin wadannan abubuwan, dama cikin duk wani kyakkyawan aiki, kada tafita saida izininsa.

    Saboda haka izinin fitar mace ko ina ne zata yana hannun mijinta ba iyayensa ba, iyaye ba su da ikon baki izinin kifita a maimakon mijinki wannan ya saɓa da koyarwar musulunci.

    Saidai bai halatta gashi miji insun samu saɓani da matarsa ta dawo kuma tanayi masa biyayya ya ce zai cigaba dafushi a kan saɓanin harta gai da shi ya ƙi amsawa wannan baya daka cikin koyarwa ta musulunci kuma laifi ne kuskure ne ya kamata mazaje masu irin wannan mugun hali suji tsoran Allah su gyara, Allah madaukakin Sarki ya ce:

    ... فَإِنْ أَطَعْنَكُمْ فَلَا تَبْغُوا عَلَيْهِنَّ سَبِيلً ...

    Idan Suka dawo sunayi muku biyayya bayan kunsamu saɓani kada kubijiro musu dawata hanyar ta musgunawa da ramuwar gayya.

    A bisa Abin da ya gabata yaharamta a kan mata sudunga fita ba tare da izinin waliyyansu ba, matan aure da 'yan mata.

    Iyay ba su da ikon baiwa surukarsu izinin fita, saidai ta bi hanyoyi na lumana da mutunci dasanin ya kamata ta karkato da zuciyar mijin nata harya hakura ya ba ta izini.

    WALLAHU A'ALAM

    Zauren Fatawowi Bisa Alkur'ani Da Sunnah, ta fahimtar magabatan ƙwarai.

    𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

    https://chat.whatsapp.com/CfDLSdXaGD00Wpxdfy2ofp

    𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

    Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

    𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

    https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi

    ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

    **************************

    Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

    Questions and Answers

    No comments:

    Post a Comment

    ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.

    HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.