Bube Mai Gandu

    Citation: BunguÉ—u, U.H. (2022). WaÆ™oÆ™in Amali  SububuAhmadu Bello University Press Limited.

    Domin samun cikakken littafi, a tuntuɓi:

    Dr. Haruna Umar BunguÉ—u
    (Sarkin Gobir Na BunguÉ—u)
    Email: harunaumarbungudu@gmail.com
    Phone: 08065429369

    Waƙoƙin Amali  Sububu

    Bube Mai Gandu

    Bube mai gandu mutumen Gidan Sani ne ta hanyar Sakkwato ta ɓangaren Isa. Yana noma hatsi sosai a kowace shekara, har wasu suna ci ta bayansa, don haka Amali ya yi masa waƙa.

     

       G/WaÆ™a : Kwananka lahiya,

    : To kuma tashinka lahiya,

    : Na tahi roƙon Ubangiji,

    : Allah ya cika man da in ga mai gandu.

     

         Jagora: Kwananka lahiya,

    : To kuma tashinka lahiya,

    : Na tahi roƙon Ubangiji,

    : Allah ya cika man da in ga mai gandu.

    ‘Y/Amshi: Kwananka lahiya,

    : To kuma tashinka lahiya,

    : Na tahi roƙon Ubangiji,

    : Allah ya cika man da in ga mai gandu.

     

         Jagora: Ka zama dutcin tsakar ruwa,

    : Ko an yi gumi ba sani yakai ba,

    : Tunda wuya ba ta kai ga mai gandu,x2

    ‘Y/Amshi: Tunda wuya ba ta kai ga mai gandu.x2

    : Kwananka lahiya,

    : To kuma tashinka lahiya,

    : Na tahi roƙon Ubangiji,

    : Allah ya cika man da in ga mai gandu.

     

        Jagora: Zamfara an ce ana kira na.

    : Na ce kowa ya dakata,

    ‘Y/Amshi: Sai na yi ziyara ga Garba mai gandu[1],

     

         Jagora: Zamfara an ce ana kira na,

    : Na ce su ma su dakata,

    ‘Y/Amshi: Sai na yi ziyara ga Garna mai gandu.

     

         Jagora: Katsina an ce ana kira na,

    : Na ce su ma su dakata man.

    ‘Y/Amshi: Sai na yi ziyara ga Bube mai gandu.

     

    Jagora: Katsina an ce ana kira na,

    : Na ce su ma su hanƙura man.

    ‘Y/Amshi: Sai na yi ziyara ga Bube mai gandu.

     

         Jagora: Gobir an ce ana kira na,

    : Na ce su ma su hanƙura manx,2

    ‘Y/Amshi: Sai na yi ziyara ga Bube mai gandu.x2

     

         Jagora: Sakkwato an ce ana kirana,

    : Na ce su ma su hanƙura man,x2

    ‘Y/Amshi: Sai na yi ziyara ga Bube mai gandu.x2

     

    Jagora: Ko kura tah haÉ—an tana maiso[2] na,

    : Ga inda nan nuhwa,

    ‘Y/Amshi: Sai na haÉ—a huska da Bube mai gandu,

    : Kwananka lahiya,

    : To kuma tashinka lahiya,

    : Na tahi roƙon Ubangiji,

    : Allah ya cika man da in ga mai gandu.

     

    Jagora: Ka kwana lahiya,

    : In kuma ka tashi lahiya,

    : Su kuÉ—É—i ba É—umi[3] sukai ba,

    : Ko da ka ba ni ba ni son su,

    : Sai mani mota da ni da yarana.

    ‘Y/Amshi: Sai mani mota da ni da yarana.

    : Kwananka lahiya,

    : To kuma tashinka lahiya,

    : Na tahi roƙon Ubangiji,

    : Allah ya cika man da in ga mai gandu.

     

     Jagora: Ka tashi lahiya lau,

    : Na ga iyalinka lahiya,

    : To kuma ni ga ni lahiya lau,

    : Su kuÉ—É—i ba É—umi sukai ba,

    : Ko da ka ba ni ba ni son su,

    : Sai mani mota da ni da yarana.

    ‘Y/Amshi: Sai mani mota da ni da yarana.

     

    Jagora: Su kuÉ—É—i ba É—umi sukai ba.

    : Ko da ka ba ni ba ni son su,

    ‘Y/Amshi: Sai mani mota da ni da yaranaa,

    : Kwananka lahiya,

    : To kuma tashinka lahiya,

    : Na tahi roƙon Ubangiji,

    : Allah ya cika man da in ga mai gandu.

     

     Jagora: Ka zama dutcin[4] tsakar ruwa,

    : Ko an yi gumi ba sani yakai ba,

    : Tunda wuya ba ta kai ga mai gandu,x2

    ‘Y/Amshi: Tunda wuya ba ta kai ga mai gandu.x2

    : Kwananka lahiya,

    : To kuma tashinka lahiya,

    : Na tahi roƙon Ubangiji,

    : Allah ya cika man da in ga mai gandu,.

     

         Jagora: Allah shi ad da duniyatai,

    : To kuma shi ad da lahiratai,

    : Ya yi makaho da mai idanu,

    : Ya yi guragu da mai ƙahwahu,

    : Kowane ya san wurin laɓewa[5] tai,

    ‘Y/Amshi: Kowane ya san wurin laÉ“ewa tai,  

    : Kwananka lahiya,

    : To kuma tashinka lahiya,

    : Na tahi roƙon Ubangiji,

    : Allah ya cika man da in ga mai gandu,

     

    Jagora: Ka zama dutcin tsakar ruwa,

    : Ko an yi gumi ba sani yakai ba,

    ‘Y/Amshi: Tunda wuya ba ta kai ga mai gandu.x2

    : Kwananka lahiya,

    : To kuma tashinka lahiya,

    : Na tahi roƙon Ubangiji,

    : Allah ya cika man da in ga mai gandu.

     

         Jagora: Ka tashi lahiya lau,

    : Bube iyalinka lahiya,

    : To kuma ni ga ni lahiya lau,

    : Su kuÉ—É—i ba É—umi sukai ba,

    : Ko da ka ba ni ba ni son su,

    ‘Y/Amshi: Sai mani mota da ni da yarana.

    : Kwananka lahiya,

    : To kuma tashinka lahiya,

    : Na tahi roƙon Ubangiji,

    : Allah ya cika man da in ga mai gandu.



    [1]  Babbar gona makekiya.

    [2]  Amai.

    [3]  Magana.

    [4]  Dutsi.

    [5]  Inda yake rayuwa da samun abincinsa.

    No comments:

    Post a Comment

    ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.

    HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.