Dawai Jikan Magaji

    Citation: Bungudu, H. U. (2023). ZaÉ“aÉ“É“un waÆ™oÆ™in mawaÆ™an baka na noma. Ahmadu Bello University Press Ltd.

    Domin samun cikakken littafi, a tuntuɓi:

    Dr. Haruna Umar Bungudu
    (Sarkin Gobir Na BunguÉ—u)
    Email: harunaumarbungudu@gmail.com
    Phone: 08065429369

    Waƙoƙin Noma

    Dawai Jikan Magaji

     

     G/ WaÆ™a: Tataushe  gamba dawai,

    : Mai zwarin daji,

    : Jikan magaji bai raga noma ba,

    : Ai in dai halin mijina ya tashi,

    : Bai san dareba,

    : Ko da wane lokaci,

    : Ya ta da batun aiki,

    : Zakin Balarabe mai gangumma,

    : Dogo baban Bala,

    : Doki kalangunka dogo,

    : ÆŠan malam uban kiÉ—i,

    : Kuma ya kyauta,

    : Mijin Ladi ya biya ni,

    : Ya biya na gode,

    : Ai Abubakari na iske,

    : Ka biya ka kyauta,

    : Bawa ya biya kan na gode,

    : Ta Baraka Allah  ya ba ku,

    : Gobe kuna  ba ni.

     

     Jagora :To ku riÆ™a da gaskiya domin Allah,

    : Da kai nike jikan magaji mai rana mugu,

    : Dawaiyye dokin noma,

    : Ai warinka[1] ba su koma batun aiki,

    : Ko gardama da kai sai ka barsu,

    : Buzu ma  shakurum baÉ—i ya É“aci,

    : Na yar rikici kai madun kurum warin daji,

    : Zaki magarya bai ra noma ba,

    : Mijin Hajo bai san dare ba,

    : Bai san dare ba,

    : Ai magaji da ranakka,

    : Allah ya taimakai ya cece ni.

     

     Jagora: Ai ni Kulu,

    : Ni kulu Hwati[2] tai kira na amsa,

    : Ai ni Kulu Hwati tai kira na,

    : Na gode Hwati ‘yar manya mutane,

    : Ta Mairin Amadu ki garaje,

    : Hwati tai komi mutane,

    : Kun ga tuhwahi[3] nan na hwati,

    : Ni kulu na gode ma hwati,

    : Ai kulu hwati tai kirana,

    : ÆŠiyah Hajiya maimuna sannu hwati,

    : ÆŠiya Alhaji na Allah hwati na yaba ta,

    : Ni kulu hwati tai kirana.

     

    Jagora: Ai to kuma na amso kiranta,

    : Tunda sabtu isa amsa isa,

    : Amma ga ÆŠan kirki mutane,

    : Amma ba Ɗan ƙo dogo ba,

    : Mai amsar sabtu machuci,

    : Abada bai tcerema zargi,

    : Ko wacce ma,

    : Haƙiƙa amsa ba musunai,

    : Abin nan ko da ya yi tcada,

    : Baya faÉ—i in ga idon ka,

    : In dai ga kunyar mutane,

    : Gidansu hwati aljannah maroƙa,

    : Na sha daÉ—i in da huti,

    : Hura ta gero ga nononta mankas[4],

    : Ai tuwo na shinkahwa namanshi mankas,

    : Ga ruwan firjin nan an aje min,

    : Ga fanka nan ta motci.

     

    Jagora: Gidansu Hwati aljannar maroƙa,

    : A gaida sabon gero taushe suna,

    : Hwati farin wata sa hasken duniya duk,

    :Abinda kiy yi mani Hajiya na yaba ki,

    : Ga tsokoki an zuba min,

    : Ga ruwan firjin nan an ake min,

    : Ga fanka nan na ta motsi,

    : Gidansu Hwati aljannar maroƙa,

    : A gaida sabon gero taushe sunah,

    : Hwati farin wata sa haske duniya duk,

    : A binda ki mani Hajiya na yaba ki,

    : Allah taimake ki da hairan sannu Hwati,

    : Hwati ta Mairin Amadu nayaba ta,

    : Ni kulu na sha daÉ—i ga hwati,

    : Ta  ba ni hwan É—ari,

    : Ta yi min É—unkin gayu mutane,

    :An yi datcam mata ta miƙa min.



    [1]  WaÉ—anda ake ‘yan shekara É—aya, sa’o’in juna.

    [2]  Suna ne na mata wato Fatima – Fati.

    [3]  Tufafi/sutura.

    [4]  Da yawa kenan ko wadatatacce.

    No comments:

    Post a Comment

    ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.

    HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.