Makada Abu Dan Kurma Maru: Wakar World Bankin Duniya

    Allahu Akbar!!! Ya yi wannan WaÆ™ar a cikin Æ™arshe - Æ™arshen shekarun 1970s  lokacin da ta hanyar Bankin Duniya (World Bank assisted Program) aka buÉ—e wani Shirin Inganta Ayyukan Gona da Raya Karkara da aka kira da (Gusau Agricultural Development Project, G. A. D. P) da Hedikwata a Gusau.
    Cikin ayyukan wannan hukuma akwai samar da kayan aikin noma na Zamani da horad da Ma'aikatan gona na zamani da bayar da bashin kuÉ—i da kayan noma na zamani ga manoma da wayar da kan su akan dubarun noma na zamani da samar da hanyoyin karkara na É“urji da inganta kiyon dabbobi da samar da tsabtataccen ruwan sha ga al'ummar karkara da sauran su. A lokacin dai ne wannan hukuma ta yi gidaje ko cibiyoyin bunÆ™asa ayyukan gona a garuruwa da Ƙauyuka daban daban musamman a yankin Sakkwato ta Gabas/Yankin Zamfara kenan. A waÉ—annan cibiyoyin ne hukumar ke kai takin zamani da iraruwan shuka ingantattu da Malaman Gona masu koyad da hanyoyin noma irin na zamani. Ta hanyar wannan hukumar ne akasarin garuruwa da Ƙauyukan da ta buÉ—a irin waÉ—an nan cibiyoyin suka samu hanyoyin motar da kafin bayyanar hukumar babu su, misali titin da ya tashi daga garin Ƙaura Namoda zuwa Birnin Magaji mai tsawon kilomita 36 da ya  tashi daga bayan babbar Tashar Motar Ƙaura Namoda babu shi, wannan hukumar ce ta Æ™irÆ™ire shi a lokacin. Shi ne mu ke kira Godaben/Titin Furojet(Project) daga sunan hukumar, (Gusau Agricultural Development Project, wanda MakaÉ—a Abu ÆŠan Kurma ya kira da Woldu Bankin Duniya Furojet ita ag gaba a amshi wannan WaÆ™ar). Kuma shi ne dai aka ci gaba da amfani da shi har ya zuwa cikin shekarun 2000s, lokacin mulkin Gwamna Alhaji Mahmuda Aliyu Shinkafi (Dallatun Zamfara) da Gwamnatin Alhaji Abdulaziz Yari Abubakar (Shattiman Zamfara) a Jihar Zamfara suka shimfida mashi kwalta.

    Sannu a hankali wannan Shirin ya samu karÉ“uwa ga al'umma har ma daga baya da ya kai wa'adin karewar shi sai Gwamnatin Tsohuwar Jihar Sakkwato (Sokoto, Kebbi, Zamfara) ta mayar da shi a matsayin Shirin ta da canjin suna zuwa( Sokoto Agricultural  and Rural Development Project, S. A. D. P) ya kuma shafi kowane sashe na Jihar. An sake canza/canja ma shirin suna ya zuwa (Sokoto Agricultural and Rural Development Authority, S. A R. D. A) sunan da yake amfani da shi ya zuwa yau.

    MakaÉ—a Abu ÆŠan Kurma Maru asalin su daga gidan KiÉ—a na su MakaÉ—a Ibrahim Gurso mai Kotso Talata Mafara ne. Wani Sarki  da aka naÉ—a a Maru(Banagan Maru) ne ya tafi da Mahaifin Abu ÆŠan Kurma daga Talata Mafara, da amincewar wan shi /yayan shi, MakaÉ—a Ibrahim Gurso zuwa Maru domin ya zamo MakaÉ—in shi. Wannan ne dalilin haihuwa da zaman Abu ÆŠan Kurma a garin Maru ya zuwa yau. Bayan rasuwar Mahaifin shi a nan garin Maru, Abu ÆŠan Kurma ya zamo Halifan shi. Ya yi KiÉ—an Sarauta da na Noma kuma shi ne babban MakaÉ—in Mutanen Kwatarkwashi dake tu'ammali da Tsuntsun nan da ake kira Maiki. Ya yi masu KiÉ—an da ake kira "Baura" da abun KiÉ—an shi da ake kira Kuwaru. Bayan rasuwar Abu ÆŠan Kurma a halin yanzu Usman ne Halifan shi (duk da yake ban san takamaiman alaÆ™ar su ba, ma'ana ko Ƙanen shi ne ko kuma É—an shi ne). Allah ya kyauta makwanci, amin.
    Daga Taskar

    Malam Ibrahim Muhammad Birnin Magaji
    ÆŠanmadamin Birnin Magaji
    Imel: birninbagaji4040@gmail.com
    Lambar Waya: 08149388452, 08027484815 

    No comments:

    Post a Comment

    ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.

    HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.