Mata Ta Gari Ke Gai Da Mijinta Ina Kwana

    1.

    Mata ta gari ce ke tashin miji

    Da asubahin fari ya sallaci Mai'giji

    Ta sa masa ruwan dumi babu turji

    Ya yi wanka da alwala yana mai ji

    Da ita a zuciyarsa ba tare da tababa ba.

    2.

    Kan ya dawo ta dafa masa shayi

    Na so da ƙauna ba ta wani shayi

    Zabinta ne daga maza dubu a layi

    'Da ba bawa ba daga cikin wasu bayi

    Na Ilahun sammai da ƙassai Ya Rabba.


    3.

    Ya ce "Salamun alaikhi ya ukhtiy"

    Ta ce "Wa alaikassalaam ya Abti

    Sannu da zuwa bugun zuciyar Ati

    Hasken ruhinta wanda ba ya latti

    Wa ya ce ba da bazarka nake rawa ba?


    4.

    Zinari ka fi azurfa balle tagulla

    A duwatsu ina wanda yai ya Dala

    Gogana ka fi kowa ko a karin hula

    Kar fa a nemi masu wasa da Dala

    Ga ni gabanka durƙushe da kuɗin Laraba.


    5.

    Wasu na zuga ni kar in gaida ka

    Burinsu ne in raina ka in sauya ka

    Alhali a gida an ce in girmama ka

    Ta su zan bi ko Manzo Nabiyyinka

    Ina masu hankali ku zo ku taya ni dubawa.


    6.

    Tunda kai sallama mijina ka fita

    Amsa maka sai na nuna bajinta

    Tabbas zan yiwa kafarka tausata

    Da Zaitun na farko daga zuciyata

    Suna so ba sa so ni dai ban ga ta zama ba.


    7.

    So suke a kama ƙirga mun maza

    Zakaru biyar sai ka ce wata kaza

    Ni ke nan kamar kalwa an baza

    A kasuwar ƙauye ƙudaje na gabza

    Ku bar ni in É—au alJannata inda ba musu ba.


    8.

    Wata ta ce wai mijinta waye shi

    A matsayi har ya isa ta gaishe shi

    Ni kuwa na ce "Ni nawa shi ne shi

    Da nake burin Allah Ya rahamshe shi

    Yai masa hisabi ba tare da wani bincike ba."


    9.

    Ya ku matanmu ku fa sani a yau

    Rayuwan nan cike fa take da hau

    Mu kiyayi ShaiÉ—an don zama lau

    Ya ishe mu izina ƙunar ranar rau

    Ba sai mun tsinci kanmu cikin da na sani ba.


    10. 

    Waƙa ce sabuwa fil cike da kashedi

    Ta Ahamadu É—an Tijjani mai muradi

    A bar fitina du mu kiyayi yaÉ—a fasadi

    Kar gidanmu asa su Walakiri yin gadi

    Gobe kiyama Allah sada mu da É—an Suwaiba

    Daga Taskar

    Malam Muhammad Tajajjini Tijjani
    Imel: mmtijjani@gmail.com
    Lambar Waya: +234 806 706 2960

    A Kiyayi Haƙƙin Mallaka

    www.amsoshi.com

    No comments:

    Post a Comment

    ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.

    HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.