TATSUNIYAR WANI MAGIDANCI DA KWARTO

     Citation: BunguÉ—u, U.H. (2021). Tatsuniyar Hausa. Ahmadu Bello University Press Limited.

    Domin samun cikakken littafi, a tuntuɓi:

    Dr. Haruna Umar BunguÉ—u
    (Sarkin Gobir Na BunguÉ—u)
    Email: harunaumarbungudu@gmail.com
    Phone: 08065429369

    Tatsuniyar Hausa

    TATSUNIYAR WANI MAGIDANCI DA KWARTO

    Gatanan - gatananku

    Wani mutum ne wanda talauci ya dame shi har ya rasa wata hanyar da zai sami sauÆ™i! Ita kuma matarsa Allah ya yi mata arziki babu abinda ta rasa. Ya nemi matar da ta ranta masa kuÉ—i ko da fam biyar ne, amma ta Æ™i ranta masa, wai don gudun kar ta bashi ya Æ™i biya, ka san halin mata masu kuÉ—i.  Amma akwai wani kwarto wanda ya matsa ma wannan mata (matarsa), an yi ta gaya masa cewa kwarto yana zuwa gidansa duk lokacin da baya nan, amma dai bai kula ba. Wata rana ya yi sallama da matarsa zai yi tafiya wajen cin rani, da jin haka sai ta sanar da kwartonta cewa “maigida zai yi tafiya”, mai gidan ya É—aure kayansa ya bi jama’ar unguwarsu da na garin yana gaya masu cewa zai yi tafiya, duk suka ce Allah ya kiyaye hanya.

    TATSUNIYAR WANI MAGIDANCI DA KWARTO

    Ko da ya bar garin sai ya sami wani loko ya É“oye, sai da ya bari dare ya raba sannan ya dawo gidansa, yana shiga cikin gidan sai ya iske matarsa tare da kwarto, sai ya ja da baya ya ce; yau kwananka ya Æ™are, sai kuwa ya danÆ™ara masa kulki tim! Kwarto ko wani motsi bai yi ba ya mutu! Daga nan sai ya ce wa matar “ni na tafi”, sai ta ce don Allah ka tsaya! Shi kuma sai ya ce “Ni yanzu zuwa nike yi wajen Maigari in shaida masa cewa kin fara kashin mutane” ba sai hankalinta ya tashi ba? Ta ce don Allah ka bari in baka hwanÉ—ari, ya ce a a shi hwan É—ari ba ta sa ya yi É“oyon mutum matacce, ta ce ina ba ka hwan É—ari biyu, ya ce “a a”, sannu-sannu dai har suka shirya da kuÉ—i masu yawa, sannan ya amince, ya ce mata “to wance kar fa in ji wannan magana ko ga wani”, ta ce “ga wa zaka ji?” “Ko ga wa zaka ji?”

    TATSUNIYAR WANI MAGIDANCI DA KWARTO

    Sai ya duÆ™a ya É—auki gawar ya fita da ita, bai tsaya ko’ina ba sai wajen wani mai ganin[1] zuma, a lokacin maigidan ya aikin yaronsa gari don ya samo masu abinci, ya jingine gawar a gindin bishiyar da suke ganin, shi kuma ya É“oye, bayan wani É—an lokaci da yaron ya dawo sai ya lura da mutum a laÉ“e a gindin iccen, sai ya gaya wa maigidansa wanda ke sama yana ganin, ya ce “kai wane ai ka ga wani mutum nan a laÉ“e yana shan zuman da kake jehowa” shi ko maigidan sai ya ce “baka buge shege?” “Sami kulki ka buge shi ni na ce” ai kuwa sai ya sa sandarsa ya bashi tim! Ba sai mutum ya faÉ—i ba? Yaron yana ganin haka sai ya ce “maigida, wai ka ga mutumen da ka ce in buga wai ya faÉ—i ya mutu!” To ka san mai ganin zuma da zuciyar tsiya sai ya ce “Æ™yale shegen cigaba da aikinka” suna cikin haka sai wancan mutumen ya fito ya ce  “a gaishe ku, wannan mutum fa?” Sai suka ce masa “wai ya zo ne ya laÉ“e muna gani yana shanye zuman, don É—ai yaro ya buge shi sai ya mutu!” Sai mutumenku ya yi farat ya ce “to! Ni kam na tafi zan je in gaya wa Maigari”, “ashe ba banza ba zumanku ya fi na kowa zaÆ™i” “ni kam na tafi”, sai maigidan ya ce “don Allah ka bari in baka hwanÉ—ari”, ya ce a a shi hwan É—ari ba ta sa ya yi É“oyon mutum matacce, ya ce “ina baka hwan É—ari biyu”, ya ce “a a”, sannu-sannu dai har suka shirya da kuÉ—i masu yawa, sannan ya amince, ya ce masu “to su wane kar fa in ji wannan magana ko ga wani”, suka ce “ga wa zaka ji?” “Ko ga wa zaka ji?” Nan take ya karÉ“i kuÉ—insa ya adana.

    TATSUNIYAR WANI MAGIDANCI DA KWARTO

    Sai ya É—auki gawar ya nufi gidan saraki wato sarkin maÆ™era, don ya san maÆ™era zuciya garesu, ya sami wani wuri ya aje gawar nan da ya É—auko, sa’annan ya ce “assalamu alaikum saraki, fito kai yi man É—waÉ—i” sai saraki ya ce “wane shege ne ke son É—waÉ—i yanzu cikin tsakar dare?” Sai ya ce “duk mai son É—waÉ—i ya bari sai da safe ni ba zan fito ba”, sai mutumen ya ce “idan baka fito ka yi man É—waÉ—i ba ina mutuwa!” Wannan maganar ta Æ™ara É“ata ma saraki rai, sai ya ce “ka daÉ—e in baka mutu ba” daga nan sai mutumenka ya É“oye. Da saraki ya ji shiru sai ya leÆ™o don ya ga ko wane irin mutum ne, sai ya taras wai har ya mutu! Sai ya fara tashe shi yana cewa “kai mai son É—waÉ—i[2], tashi in gyara maka ka tafi gida”, shi kuma sai Æ™ara langaÉ“ewa yake yi, da ma kun san yadda abin yake. Ai sai mutumenku ya É“ullo ya ce “Allah dai ya sa lafiya saraki a tsakar dare da wani” ko da saraki ya ji shi, sai ya ce “kai ni wani mutum ne mai shegiyar zuciya ya zo wai in yi masa É—waÉ—i, na ce ban fitowa cikin dare, sai ya ce in ban fito ba zai mutu, kuma na ce ban fitowa sai kuwa ya kwanta ya mutun!” Sai mutumenku ya yi ajiyar zuciya ya ce “to!” Ni kam na tafi zan je in gaya wa Maigari, “ashe ba banza ba Æ™irarka ta fi ta kowa kyawo” “ni kam na tafi in gaya wa Maigari”,

    TATSUNIYAR WANI MAGIDANCI DA KWARTO

    Sai saraki ya ce “don Allah ka bari ina baka hwan É—ari”, ya ce “ina baka hwan É—ari biyu”, ya ce “a a”, sannu-sannu dai har suka shirya da kuÉ—i masu yawa, sannan ya amince, ya ce masu to su wane kar fa in ji wannan magana ko ga wani, suka ce “ga wa zaka ji?” “Ko ga wa zaka ji?” Nan take ya karÉ“i kuÉ—insa ya adana.

     

    Ko da ya É—auki gawarsa bai tsaya ko’ina ba sai a masallaci, da zuwansa sai ya iske irinladanan nan masu sakkon kiran sallah, ladanin masallacin har ya hau wurin kiran sallah, ya fara kiran sallah sai ya ce ga wata sadaka ta hatsi ko a yi maka gumba. Sai kuwa ladan ya sauko ya yanke kiran sallar ya karÉ“i sadakar ya juya ya kai gida ya ajiye sannan ya dawo ya yi wani kiran sallar. Ladan bai koma ba sai da aka Æ™are sallah. Yana zuwa sai ya gaya wa matarsa cewa “wai wani bawan Allah na haÉ—u da shi ya ba ni sadakar hatsi, ai kuwa sai ta taso ta kama masa aka kwance. Shi kuma mutumen yana laÉ“e har ya ji sun fara sallallami sai ya shigo, ya ce sannunku ladan injin dai lafiya? Sai ladan ya yi masa bayanin cewa wai wani bawan Allah ne ya ba ni sadakar hatsi sai yanzu da muka kwance ashe ba hatsin ba ne gawa ce!

    TATSUNIYAR WANI MAGIDANCI DA KWARTO

    Sai mutuminku ya ce to ni dai sai an jima, ashe ba banza ba ka fi kowane ladan zaÆ™in murya, na tafi in gaya wa Maigari. Sai ladan ya ce don Allah ka tsaya, sai shi kuma ya ce in tsaya mi zaka ba ni?  ya ce ina ba ka hwan É—ari biyu”, ya ce a a, sannu-sannu dai har suka shirya da kuÉ—i masu yawa, sannan ya amince, da ladan ya ce ma matarsa ta kawo kuÉ—in adashin da suke yi don a haÉ—a a sallame shi, aka tattaro duk kuÉ—in gidan nan aka biya. Daga nan ya ce masu “to su wane kar fa in ji wannan magana ko ga wani”, suka ce “ga wa zaka ji?” “Ko ga wa zaka ji?” Nan take ya karÉ“i kuÉ—insa ya adana.  Da ya É—auki gawar bai tsaya koina ba sai bakin gulbin garin saboda haske ya fara an fara buji-buji, ya kuma yi sa’a gulbin ya É—ebo ruwa, sai ya jefa gawar tsundum! Gawar Kwarto ta nutse ruwan ya tafi da ita. Sai mutumen ya koma gidansa ya cigaba da tafiyar da rayuwarsa kamar kowa, cikin walwala kuma babu mai biyarsa bashi.

    Ƙungurus kan kusu, kusu baya ci na, sai dai in ci kan ɗan banza, na yi tun tuɓe da gurun kaza, na faɗa rijiyar zuma na dabshe baki da man shanu, alkaki ya tsamo ni.

    Tambayoyi

    1.                  Wane dalili ne ya sa mijin matar nan ya yi tunanin fita ya je wurin cin rani?

    2.                  Mutum nawa ne wannan mijin matar ya zalunta a cikin wannan tatsuniyar?

    3.                  WaÉ—anne irin darusa ne aka koya daga wannan tatsuniyar?



    [1]  ÆŠibar zuma daga wurin da ya tara shi.

    [2]  KuÉ—ar wasu kayan aiki musamman na noma.

    No comments:

    Post a Comment

    ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.

    HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.