Waƙar Rabon Gado: Ta Malam Ibrahim Halilu Marinar Tsamiya

     Citation: Bunguɗu, U.H. (2021). Bara da wasu waƙoƙin bara a ƙasar HausaAhmadu Bello University Press Limited.

    Domin samun cikakken littafi, a tuntuɓi:

    Dr. Haruna Umar Bunguɗu
    (Sarkin Gobir Na Bunguɗu)
    Email: harunaumarbungudu@gmail.com
    Phone: 08065429369

    Bara da wasu waƙoƙin bara a ƙasar Hausa

    Waƙar Rabon Gado: Ta Malam Ibrahim Halilu Marinar Tsamiya

    1. Mu gode Jalla wanda yaw wadata,

     Ga al’amurrar duka bai buƙata.

    2. Mu sallama ma Musɗafa Manzommu,

     Da Alu har Sahbu su agaje mu.

    3. Zani ƙasida ta rabon Mirasi,

     Ga ɗakuna shidda bisa ga nassi.

    4. Ka san gidajen da ka ɗaukat gado,

     Kowane ɗaki suke ka ji ƙasida.

    5. Lazimci Larbi na cikin Risala,

     Tsaya ka gane shi ka bar kasala.

     6. Haba da baz bi shi ka san ashabu,

     Ka san waɗanda za ka ba nisabu.

    7. Lura ka gane ma’abuta nisfi,

     Guda biyat na ka riƙa da ƙarfi.

    8. Ka sa miji ka sa ɗiya da sulɓi,

     Ka sa ɗiyat ɗa ita ag ga larbi.

    9. Da ‘yar’uwa Shaƙiƙiya kawo ta,

     Ko ita nisfi taka son a ba ta.

    10. Da ‘yar’uwa jahat uba ka falka,

     Ka ji biyat sun cika babu shakka.

    11. Sa ma’abuta rubu’i su biyu na,

     Miji da mata da yawa na sunna.

    12. Sa ma’abuta sumuni zaujatu,

     Su at guda ɗai ga ƙidan siƙatu

    13. Su ma’abota sulusani su ko,

     Su duka na lura da su ka sakko

    14. Ɗiyan tsatso sai bi da bintani,

     Ɗa biyu jahat da ka biɗo ukhtani

     15. Shaƙiƙatani babu duk khilafa,

     Sulusani at na su riƙe ka ƙarfafa

     16. Da ‘yan uwa biyu ga jahat uba suke

     Ukhtani ke nan ka tsare ka warke

     17. Su huɗu ke nan ga ƙida ka gane

     Yi ijtihadi ka iya su kowane

     18. Sa ma’abota sulusi su biyu na,

     Uwa da isnaini li’ummi ka tuna

     19. Sun cika daidai sulusi at,

     Lura da su ba ka da mai kaushe su

     20. Sa ma’abuta sudusi guda bakwai,

     Kar fa ka sake su riƙe su daidai

     21. Zana kasa uwa rabonsa,

     Duk sudusi anka fitas ka ba su

     22. Ka ba ɗiyat ɗa uwat uba duka,

     Uwat uwa sa ta ga ka duka cika.

     23. Da ‘yar uwa jahat uba da ɗan’uwa

     Shi ko li’ummi bari raunanawa

     24. Sun cika daidai bisa wanga larbi,

     Kway yi shi ya tsira ga masu albi

     25. Allah shi haushe mu bisa sawaba,

     Da godaben Annabi mai muhibba

     26. Na cika waƙa ta batun mirasi,

     Allah ka tara mu cikin firdausi

     27. Mai tambayal Naziru Ibrahimu,

     Yay yi ta sattaru rufe laifinmu

     28. Mu yo salati inda ɗan Amina,

     Da Alu har sahabu da tabi’ai.

    No comments:

    Post a Comment

    ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.

    HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.