Wakokin Noma Na Audu Dangunduwa

     Citation: Bungudu, H. U. (2023). Zaɓaɓɓun waƙoƙin mawaƙan baka na noma. Ahmadu Bello University Press Ltd.

    Domin samun cikakken littafi, a tuntuɓi:

    Dr. Haruna Umar Bungudu
    (Sarkin Gobir Na Bunguɗu)
    Email: harunaumarbungudu@gmail.com
    Phone: 08065429369

    Waƙoƙin Noma

    Waƙoƙin Noma Na Audu Ɗangunduwa

    Waƙoƙin Noma Na Audu Ɗangunduwa 

    Taƙaitaccen Tarihin Audu Ɗangunduwa

    Sunansa zananne shi ne Abdullahi, an haife shi ne a garin Tungar Ɗangudo wani ƙauye a ƙaramar hukumar Talatar Mafara  a shekarar dubu ɗaya da ɗari tara da ashirin daidai (1920). Audu ya gaji kiɗa ne ga mahaifinsa Alhaji Abdullahi Ɗangunduwa Kagarar Morai domin shi ma makaɗi ne sananne a yankin bakiɗaya.

    Magidanci ne matarsa ɗaya mai suna Amina, ‘ya’yansa tara maza shida mata uku. Akwai daga cikin ‘ya’yan nasa Muhammadu Sani da Ya’u da Shehu da Nasiru da Mustafa da Kuma Yunusa, su kuma matan su ne Aisha (babba) da Rabi da kuma Aisha (ƙarama). Yana yin kiɗe-kiɗen noma da na sarakuna. Kayan kiɗansa kalangu ne da wanim lokaci kotso na kiɗin sarakuna. ‘yan amshinsa su bakwai ne, akwai Ya’u da Hussanida Sa’idu daAbubakar da Muhtari da Muhammadu Nagido da kuma Ummaru Guga, sai kuma Muhammadu Sani wanda shi ne ya jagoranci ƙungiyar bayan rasuwar tsohon nasa.

    No comments:

    Post a Comment

    ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.

    HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.