Wakokin Noma Na Bako Rugum Kiri

     Citation: Bungudu, H. U. (2023). Zaɓaɓɓun waƙoƙin mawaƙan baka na noma. Ahmadu Bello University Press Ltd.

    Domin samun cikakken littafi, a tuntuɓi:

    Dr. Haruna Umar Bungudu
    (Sarkin Gobir Na Bunguɗu)
    Email: harunaumarbungudu@gmail.com
    Phone: 08065429369

    Waƙoƙin Noma

    Waƙoƙin Noma Na Baƙo Rugum Ƙiri

    Baƙo Rugum makaɗin noma ne wanda yake amfani da gangar noma wato irin wannan da ake kira ta guiwa ko tallabe. Kuma ‘yan amshinsa mata ne matansa ne na aure su uku suke tafiya tare da shi suna yi masa amshin.

    Taƙaitaccen Tarihin Rayuwarsa

    An haife shi a shekarar 1873 ne a garin Gada Ƙiri ta jihar Sakkwato. Sunansa na yanka shi ne Salihu, ya gaji kiɗan ne daga mahaifinsa wanda sunansu ɗaya da shi wato Salihu wanda yake makaɗin yaƙi ne daga baya ya koma yana kiɗin fatake. Mahaifiyarsa kuwa sunanta Inno, ’yar asalin garin Gada Ƙiri ce. Matan aurensa uku ne da Haddi da Maimuna da ‘Yat tunga. Bayan ‘yan amshinsa wato matansa akwai wasu maza su biyar masu yi masa kiɗi a lokacin da yake waƙoƙinsa, su ne Ummaru da Mamman Ɗanhulai da Audu da Jabba da kuma Roro. Babu wata waƙa da yake yi daban in banda waƙoƙin noma.

    Ya rasu yana da shekara ɗari da talatin da huɗu a shekara ta dubu biyu da bakwai (2007), yana da shekara goma sha shida da rasuwa kenan a yanzu (2023).

    No comments:

    Post a Comment

    ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.

    HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.