Addu'ar Da Idan Kayi Allah Zai Amshi Buqatarka

    TAMBAYA (19)

    Dan Allah adduar biyan bukata fah

    AMSA

    Annabi SAW ya ce duk wanda yayi addu'ar ma'abocin kifi (Annabi Yunus AS) ya roqi Allah wata buqata to za a biya masa

    Lokacin da Annabi Yunus yayi hijira daga garinsa batareda umarnin Allah SWT sai ya shiga jirgin ruwa, akayi kuri'a silar tambal-tambal da ruwan tekun yake, kuri'a fa fada kan Annabi Yunus, mutanen jirgin suka wullasa cikin tekun

    Ya nutse can kasa, kifi ya hadiyesa kamar yanda Qur'ani ya tabbatarda faruwar hakan:

    ( فَاصْبِرْ لِحُكْمِ رَبِّكَ وَلَا تَكُن كَصَاحِبِ الْحُوتِ إِذْ نَادَىٰ وَهُوَ مَكْظُومٌ )

    القلم (48) Al-Qalam

    Sabõda haka, ka yi haƙuri da hukuncin Ubangijinka, kada ka zama kamar Ma'abũcin kĩfi, alõkacin da ya yi kira, alhãli yana cike da hushi.

    A lokacin da ya tuno musabbabin faruwar hakan sai ya koma ga Allah SWT:

    ( وَذَا النُّونِ إِذ ذَّهَبَ مُغَاضِبًا فَظَنَّ أَن لَّن نَّقْدِرَ عَلَيْهِ فَنَادَىٰ فِي الظُّلُمَاتِ أَن لَّا إِلَٰهَ إِلَّا أَنتَ سُبْحَانَكَ إِنِّي كُنتُ مِنَ الظَّالِمِينَ )

    الأنبياء (87) Al-Anbiyaa

    Kuma mai kifi a sã'ad da ya tafi yanã mai hushi, sai ya yi zaton cwa ba zã Mu ƙuƙunta masa ba. Sai ya yi kira a cikin duffai cwa, "Bãbu abĩn bautãwa fãce Kai. Tsarki ya tabbata a gare Ka. Lalle ne nĩ, na kasance daga azzãlumai."

    Nan take Allah SWT ya amsa roqon bawanSa harma ya ce:

    ( فَلَوْلَا أَنَّهُ كَانَ مِنَ الْمُسَبِّحِينَ )

    الصافات (143) As-Saaffaat

    To, ba dõmin lalle shi ya kasance daga mãsu tasbĩhi ba,

    ( لَلَبِثَ فِي بَطْنِهِ إِلَىٰ يَوْمِ يُبْعَثُونَ )

    الصافات (144) As-Saaffaat

    Lalle dã ya zauna a cikin cikinsa har ya zuwa rãnar da zã a tãyar da su.

    An karbo daga Abu Dharr al-Ghifari (RTA) ya ce, Annabi SAW ya ce: "Kada kuyi tunanin kunfi Yunus Ibn Matta (AS). Ya kira Ubangijinsa ya ce: "Bãbu abĩn bautãwa fãce Kai. Tsarki ya tabbata a gare Ka. Lalle ne nĩ, na kasance daga azzãlumai.

    (Sunan Abu Dawud: 3871 da kuma As-Sifah al-Jami'ah na Imam al-Bayhaqi)

    Sannan kuma akwai lokutan amsar addu'a. Kamar lokacin da ladan ya kammala kiran sallah

    عن أنس بن مالك رضي الله عنه قال رسول صلى الله عليه وسلملا يرد الدعاء بين الأذان والإقامة».

    رواه أبو داود و الترمذي

    An karbo daga Anas Dan Malik Allah ya kara yarda da shi ya ce Manzon Allah صلى الله عليه وسلم ya ce: «Ba'a maida addu'a tsakanin kiran sallah da tayar da sallah»

    (Abu Dawud da Tirmiziy ne suka rawaitoshi)

    Don haka da zarar kinji ladan ya kira sallah saiki maimaita abin da ya ce (saidai idan ya ce Hayya alal fala da Hayya alas sala ke kuma zakice "Lahaula wala quwwata illa billah) bayan ya gama saiki karanta "Lailaha illa antas subhanaka inni kuntu minazzalimin" ki yi salatil Ibrahimiyya sannan ki roqi dukkan abin da kike so

    Wallahu ta'ala a'alam

    Amsawa:

    Usman Danliti Mato (Usmannoor_As-salafy)

    https://chat.whatsapp.com/EbkKRXdFzNu4F8aQZbZ1Vx

    Question and Answers in Islam

    No comments:

    Post a Comment

    ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.

    HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.