Alamomin Balaga

    𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

    Game da yarinyar da ba ta fara haila ba amma ta fara kirgan-dangi, kuma da yaron da bai yi mafarki ba amma ya fara warin hammata, shin za su rama azumin Ramadan da suka sha ko ba za su rama ba?

    𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

    Masana sun ce: Alamun balaga a wurin yaro su ne:

    1. Fitar maniyyi daga gare shi a cikin barci ko a farke.

    2. Tsirar gashi mai ƙarfi mai duhu a mararsa da hammatarsa.

    3. Fitowar gashin gemu da saje da gashin baki a fuskarsa.

    4. Buɗewar muryarsa.

    5. Bayyanar waɗansu ƙurajen pimples a fuskarsa.

    6. Samun warin jikinsa (warin balaga).

    A wurin yarinya kuwa alamun su ne:

    1. Samuwar jinin haila daga gare ta.

    2. Bayyanar nono a ƙirjinta, wanda kuma yake cigaba da girma kaɗan-kaɗan.

    3. Tsirowar gashi mai ƙarfi mai duhu a hammatarta da mararta.

    4. Bayyanar waɗansu ƙurajen Pimples a fuskarta.

    5. Sauyi a cikin gashin kanta, ta yadda yakan ƙara zama maniimci mai santsi da laushi.

    6. Samuwar warin jiki (watau: Warin Balaga).

    7. Ƙarin faɗin ƙugunta.

    8. Fitar maniyyi a cikin barci ko a farke.

    Don haka, duk wanda ya ga ɗaya daga cikin waɗannan alamomin sai ya kara kulawa da addininsa sosai.

    Kodayake wasu Malamai sun nuna cewa babbar alamar balaga a wurin namiji ita ce fitar maniyyi, a wurin mace kuma fitar haila ce, amma dai abu mafi-kyau shi ne su rama duk azumin Ramadan da suka sha kawai, domin fita daga matsala a Lahira. 

    WALLAHU A'ALAM

    Sheikh Muhammad Abdullaahi Assalafiy

     

    Zauren Fatawowi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...

    𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

    https://chat.whatsapp.com/Du5LNx31U9hDi6RQbbrzgW

    𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

    https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi

    𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

    Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

    ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

    **************************

    Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

    Question and Answers in Islam

    No comments:

    Post a Comment

    ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.

    HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.