GOBIR TA BAWA GAMBUN HAUSA KURYA GANGAR MUTUWA

    Takardar da aka gabatar domin taya Farfesa Muhammad Ahmad Sabon Birni samun kujerar Farfesa a fannin Paediatrics a Makarantar Ilmukan Kiyon Lafiya (College of  Health Science), Jami’ar Usmanu ÆŠanfodiyo, Sakkwato ranar Lahadi 29/1/2023 a Giginya Hotel,Sakkwato da Æ™arfe 11:00am na safe

     

    Aliyu Muhammad Bunza
    Sashen Koyar da Harsunan Nijeriya
    Jami’ar Usmanu ÆŠanfodiyo, Sakkwato
    Waya: 0803 431 6508
    Ƙibɗau: mabunza @yahoo.com

     Tsakure

    Hausawa na cewa: “Kowane tsuntsu kukan gidansu yake yi.” Kowace irin al’umma magabatanta ke jawo mata girma ko akasinsa. Na tabbata taron Æ™asa-da-Æ™asa da Jami’ar Sakkwato ta yi kan Daular Gobir 2021 masana ba su raga wata babbar kafa da É—alibai irinmu za su leÆ™a ba. Don haka, na É—an hango wani bagire da ya shafi uban tafiyar kansa wato Sarkin Gobir Malam Sheikh Umar Bawa Jangwarzo. Na yi amfani da tattaunawa da Gobirawa da Fulani da Katsinawa da Kabawa, kuma na ratsi ayyuka wallafaffu da waÉ—anda ba a wallafa ba kan Gobir da Gobirawa da Sarkin Gobir Umar Bawa. Na amfana da ayyukan da suke cikin google na kuma ratsi kundin tarihin Daular Gobir da Jami’ar Usman ÆŠanfodiyo ta wallafa (2021). Na gano ba a samu wani fitaccen aiki da aka yi a kan sunan Sarkin Gobir Malam Sheikh Umar Bawa Jangwarzo ba. Daga cikin Sarakunan Gobir fiye da (300) babu wanda sunansa ya kere na Sarki  Umar Bawa. Na yi duba cikin natsuwa kan sunan BAWA a Hausance, kana na warga ga muhallin ‘jan” launi a adabi da al’ada. Na kwakkwafe bayanina a kan kalmar “gwarzo”. Binciken an gina shi kan fasula (13) haÉ—a da gabatarwa da naÉ—ewa. Nazarin ya gano sunan da sarautarsa da kasancewarsa mai martaba uku, É—an sarauta, sarki, malami, da gawurtaccen jarumi, su suka ba shi muÆ™amin da ba basaraken da ke da shi a Gobir da Æ™asashen da ke kewaye da ita, wato JANGWARZO. Kirarin “Gobir gidan faÉ—a” ta daÉ—e da shi, amma zamanin Sarkin Gobir Malam Umar Bawa aka yi wa kirarin Æ™ari da cewa: “Gobir Ta Bawa Gidan FaÉ—a”.YaÆ™e-yaÆ™en Gobirawa shi ya ba su ‘yancin cin moriyar Æ™asarsu ta kasance wani gambu da katangar  Æ™arfe ga sauran Æ™asashen Hausa. Hasashen bincikena, ina kyautata zaton ranar LARBA aka haifi Sarki Bawa, saboda sanin jumu’ar da ke albarka tun ranar Larba ake ganewa; bisa ga kirarin Bahaushe na, Larba ta Bawa ranar samu kowa ya samu gare ki, sai ya Æ™ara. Allah Masani.

    Gabatarwa

    Al’adar bincike ita ce, samar da wata ‘yar gudunmuwa ga abin da ya gabata domin Æ™ara rage zango. Gobirawa da tarihin kakaninsu sananne ne a adabin baka da rubuce-rubucen tarihi cikin Ibrahimiyanci (Hebrew) da Girkanci, da Larabci, da Ingilishi da sauran harsunan Afirka. Wannan takarda É—an tsokaci za ta yi ga É—an wani bagire da bai sha lugude sosai daga masana ba. Irin yadda Gobirawa suka mamaye duniyar baÆ™ar fata ko’ina sun kafa sansanin gari ko tunga. Sarautunsu suka kai wuraren da faÉ—in Æ™asarsu bai kai ba. YaÆ™e-yaÆ™ensu suka kai nesa ga kadadar Æ™asashen da suke iko. Famarsu ta mamaye su nan magabatansu da mabiya bayansu a tarihi ka ce, babu wata zuriya daga cikin zuriyar mazauna Sudaniyya in ba Gobirawa ba. Babban abin mamaki sunan Sarkinsu BAWA ya mamaye tarihin sarakunan Sudaniyya, ka ce duk daulolin Sudaniyya Æ™arÆ™ashin ikon Sarki Bawa suke. MaÆ™asudin wannan ‘yar takarda kallon sunan sarki Bawa da abubuwan da sunansa ya Æ™unsa, tare da fayyace amsa amon sunansa “JAN GWARZO” cikin biyar diddigin adabi, al’ada, da nahawu.

    Fashin Baƙin Matashiya

    Kalmar da ta limanci matashiyarmu ita ce “Gobir”. Masana da dama sun tofa albarkacin bakinsu a kan ta. A ganin Gobirawa daga GUBUR take wato tsohon wurin da suka baro suka yo hijira. Wasu masana na ganin daga kalmar “Kobir” ko “Kubir” ne mai ma’anar “Tagulla” (Coper). Idan ma aka ce daga kalmar “Coper” ce ta Ingilishi akwai abin cewa a ciki a nahawun tarihi. Masu danganta ta da daÉ—aÉ—É—iyar ginan nan ta Katsina wato “Gobarau” ba jifa cikin tudu suka yi ba. Na daÉ—e ina tunanin, anya! Hausawa ba daga bakin Adarawa ko Azbinawan Agades suka ji furucin suka ara ba? A Bahaushen tunani na tarihin tarihi ya kamata mu fara jinjina nauyin wasu kalmomi masu alaÆ™a da sunan irin su: Gobara, goriba, gurbi, da sauransu. Yanki na biyu shi ne, “Ta Bawa” Ba Bawa ne Sarkin Gobir na farko ba, ficensa da kere da ya yi wa sauran sarakunan Gobir aka danganta Æ™asar gaba É—aya da sunansa”.”Ta Bawa”. A nahawu, samun harafin “ta” gabanin suna yana tabbatar da kasancewar sunan na jinsin “mace” ne, ba a haÉ—e su da “Bawa”, in an yi sai ya ba da sunan mace “Tabawa”. A gargajiyance gambu shi ne tsaro ga gari, da gida, da É—aki, in babu shamakin gambo babu tsaro ga muhalli. Gobir ita ce, tsaro ga Æ™asar Hausa.

    Daga gangan na kawo kirarin Gobirawa na fama da ake yi musu: “Kurya Gangar Mutuwa”. Kurya turun kiÉ—a ne da ake haÉ—awa da duma wajen kiÉ—in yaÆ™i da artabu da tayar da maza daga barcin raggwanci. Kurya ta fi duma murya mai shiga zuciya da yamutse rayuwa da gigita gwaraje da gawurtattu. Kurya ba ta barin maza su mazaya sai dai a mutu har liman tare da mai kiÉ—in da kuryarsa duka. Da wuya a ji muryar kurya babu gawa kwance domin muryarta cewa take yi:

    : Komi taka zama ta zama!

    : Komi taka zama ta daÉ—e!

    Haka Gobirawa suke a fagen daga in nasara, in mutuwa. Dubi yadda askarawan Satiru na ƙasar Ɗancaɗi ta Boɗinga Gobirawa (Wazirin Boɗinga: 2023) ke atisayen yaƙi da Turawan Biritaniya a (1906) suke cewa:

    Ku sa kiÉ—i mazaizai mu gani,

    Ko can gida faÉ—a mun ka sani,

    Ba mu san gudu ba sai dai a mutu.

     

    Idan fagen artabu ya yi cin alewar kuturu, kurya ake jefawa tsakanin maÆ™iya mazaje su je su karÉ“o ta mai rabon ganin baÉ—i shi gani (Kwatantagora: 1999). Haka idan an rufe birni an hana abokan gaba shiga, makaÉ—in kurya  yake jefawa tsallaken Æ™yauren Æ™ofar birni ta je can ta tarar da abokan gaba, su kuwa dakarun gaba sai tsallakar Æ™yaure da ganuwar gari, a riski abokan gaba cikin garinsu a ce musu aljanna gafara wuta salamu alaikum. Rashin tsoron Gobirawa da mayar da mutuwa tobashiyarsu, da rungumar takaici domin kunya ta san in da dare ya yi mata, shi ya sa ake yi musu kirari da “Kurya Gangar Mutuwa”.

    Gurbin Sunan “Bawa” Cikin Sunayen Hausawa

    Tunanina a wannan bincike in tsaya kan sunan Sarki Bawa Jangwarzo a kadadar al’adar Bahaushe. A Æ™asar Hausa, kalmar “bawa” tana da fassarori da dama. Daga cikin fassarorin akwai:

    1-    Bawa daga cikin bayin sarki, ba dole sai bawa na haÆ™iÆ™a ba, a’a ha, mai cika wa sarki aiki, da ya ce, “a yi” an gama. Don haka ake ce wa “dakarun yaÆ™i", bayin sarki.

    2-    Akwai bawa kamamme da aka rinjaya fagen artabu, ko aka sayo kasuwa, ko ya gaji bauta daga iyayensa, ko aka bautar da shi da               Æ™arfi-da-yaji a Æ™abilance ko a yaudarance da sunan addini.

    3-    Akwai “bawan gona” wanda aka ba gona ya noma a shekara ya biya “tirkici” in ya yi dami goma ya ba da É—aya, in ya yi É—ari ya ba da goma haka dai zuwa. A Sakkwato da Kabi ana ce da su “Runji”, muna da “Runjin Sambo” a misali.

    4-    Akwai “bawan bashi” wanda ya sha ta fi cikinsa, sai a riÆ™e shi a matsayin bawa, ya dinga Æ™wadago ga mai bashi har sai wahalarsa ta biya murgunsa.

    5-    Akwai “Bawa” wanda ke bi wa mata ga haihuwa a wasu wurare a ce da shi Gambo.

    6-    Akwai “Bawa” wanda aka haifa ranar “Larba” ana sa masa suna “Bawa” domin neman albarkar ranar. Magabata sun ce, an halicci kowane haske ranar Larba don haka ko karatun zaure ranar Larba ake farawa, kuma akwai kuÉ—in bulala da ake biya ranar kowace Larba. Dalilin Hausawa ke nan na yi mata kirari da:

    Larba ta Bawa ranar samu,

    Kowa ya samu gare ki sai ya ƙara.

    7-    Na Æ™arshe akwai laÆ™abin da ake yi wa yara na neman É—aukaka irin ta “Sarki Umar Bawa Jangwarzo” kowane Bagobir na son a samu Bawa gidansa. Haka kuma kowane Bahaushe idan ya ji irin É—aukakar Bawa da tagomashinsa yakan so ya sa wa yaronsa Bawa domin takwara ga JANGWARZO.

            A taÆ™aice za mu ce, Sarkin Gobir Bawa Jangwarzo sarki ne, É—an sarki, jikan sarki, don haka hasashe da muka gabatar a lambobi na (1-4) ba za su kusace shi ba. Ala tilas yana cikin hasashe na (5-6) wanda shi ya haifar da hasashen na (7). Sunan Sarkin Gobir Umar Bawa Jangwarzo ya É“ace gaba É—aya sai dai ka ji an ce: Bawa ko Malam Bawa ko Jangwarzo, a Jamhuriyar Nijar in ba Malam Bawa ka ce ba, ba a gane da Sarki Bawa kake domin Malami ne kuma Sarki ne gaba da baya, a ji sarki, a ga sarki. Malam Bawa ya yi tasiri sosai a Æ™asar Hausa ba ma ga Gobirawa kawai ba, a’a a tarihin Æ™asar Hausa. Ga wasu misalai biyu don tabbatarwa:

    1-    A Sakkwato hanyar zuwa mazaunin din-din-din na Jami’ar Usmanu ÆŠanfodiyo Sakkwato akwai Kantin magani gawurtacce sunansa JANGWRZO CH.

    2-    A MaraÉ—i akwai Hotel babba sunansa JANGWARZO kundin PhD Hausa da aka fara yi a fannin waÆ™oÆ™in Addini a duniyar Æ™asar Hausa, a Jami’ar SOAS Ingila, wanda Prof. M. Hisket ya yi, (1975) da aka wallafa shi, waÆ™ar Yabon Sarkin Gobir Malam Bawa Jangwarzo aka buga a bangonsa.

    Danganta Bawa da Launin “Ja” a Bahaushen Tunani

    Tunanin wannan bincike feÉ—e tunanin Gobirawa na saka wa Sarkin Gobir Malam Umar Bawa sunan  JANGWARZO, na ga ya fi kyau mu fara da kalmar “Ja” a Bahaushen tunani. Launin “Ja” kirari ne ga zarumi saÉ“anin wasu launuka da ba shi ba. Me ya sa ba su ce, fari ko kore ko shuÉ—i da sauransu? Dalili shi ne, fari na shiga cikin yabo amma ba ya É—aukar kirari, haka nan sauran launuka. Launin “baÆ™i" na É—aukar kirari da yabo amma ba na ma’abota É—aukaka da alfarma ba. Sauran launukan da muke da su duka ba sa É—aukar kirari da kambama ma’abota alfarma kamar yadda “ja” yake yi a al’adance. Ma’aunin kalmar “ja” ko in ce launin “ja” a dubi ma’auninta:

    1-    Ja

    2-    Ja

    3-    Jajaye 

    4-    Jajaja 

    5-    Jajircewa  

    6-    Jajirtacce

    7-    Jajirtattu

    8-    Jajir

    9-    Jajibiri

    10-Jaji

    -         Ai Abubakar jan namiji ne.

    -         Garba ba wasa an ja ya ja.

    -         Matan Buba jajaye ne.

    -         Ya damu fuskarsa ta yi jajaja.

    -         MayaÆ™an masu jajircewa ne.

    -         Bawa jajirtaccen namiji ne.

    -         Dakarun jajirtattu ne ba wasa.

    -         Dubi idanun mutum kamar maye jajir ba su da fari.

    -         Kwananmu bakwai ranar jajibirin kokuwar muka isa.

    -         Fargar jaji

         Bahaushe ya yi tunani mai zurfi wajen zaÉ“ar launin “ja” saboda sabawarsa da ‘ya’yan ita ce da yake ganin kai matuÆ™a ta ninarsu ja suke yi daga cikin su akwai:

    -         Kaiwa

    -         Goriba

    -         Giginginya

    -         Tonka

    -         Gauta

    -         Wake

    -         GyaÉ—a

    -         Masara

    -         Yalo

    -         Janzakara

          Idan aka kula, yadda duk launin “ja” ya kasance ya kai matuÆ™a ga nunarsu, haka nan ake ganin kirari da launin ja shi ne matuÆ™a ga jarumi. Dubi yadda kalmar “ja” ta yi naso a zantukan hikima da kirare-kiraren Bahaushe:

    -         Jan kara jan zaÆ™i (in ji masu rake).

    -         Jan ido alamun namiji.

    -         Kowane gauta ja ne, sai in ba ji zafin rana ba.

    -         Jan aiki.

    -         Aiki ja.

    -         Jar wuta ita ce danja.

      A tunanin waÉ—annan zantukan hikima da karin magana launin ‘ja’ ba Æ™aramar daraja yake da ita ba, musamman a fagen yi wa gwarzo kirarin da ya dace da Æ™oÆ™arinsa. A kowanne daga cikinsu duk irin launin da aka sa ma’anar ba ta fitowa yadda za a buÆ™ace ta. A adabin zaruntaka na kambama gwaraje da cicciÉ“a su, za mu ga launin “ja” na da tasiri ciki sosai, misali a dubi waÉ—annan zantuka:

    -         Jini da  jini, janjan (mabuÉ—in karafkiya a goshin yaÆ™i)

    -         JarÆ™aniya (kalmar Æ™undumbala)

    -         Jannasuri (Maciji gawurtacce na cikin suri)

    Launin “Ja” a Tatsuniya da Wasanni

    Daga cikin daÉ—aÉ—É—un adabin gargajiya akwai tatsuniya da wasannin yara. Tatsuniya da wasannin yara wasu makarantu ne da kowane É—alibin ilmi ya kamata ya ziyarta idan yana son biyan tushen diddigin kowane irin abu da ya shafi al’adar ma’abotanta. Daga cikin tatsuniya muna da:

    Ja ya faÉ—i, ja ya É—auke

    Giginya ta faÉ—i É—an Bafulatani ya É—auke.

              Haka kuma a cikin wasannin yara akwai wasar da ake yi:

    Jagora: Jini da jini.

    Amshi:  Janjan.

    Jagora:  Rago da jini.

    Amshi:  Janjan.

    Jagora: Kifi da jini.

    Amshi:  Janjan.

    Jagora:  Masara da jini.

    Amsa:  Yara za su yi tsit! Wanda ya ce jan jan sai duka.

    Wasa ne na maza da maza, don haka aka É—auki launin ‘ja” na jini aka sarrafa, wanda duk ya yi kuskure zai sha duka sosai ba mahani. A taÆ™aice, jarunta ta yi amo cikin waÆ™e-waÆ™en yara da ake sarrafa launin “ja”. Dubi wani wasa na nuna Æ™warewa ga harshe da matasa ke sarrafa launin “ja” a ciki:

    Kai jan mutumin can

    Ka É—auki jar sandar can

    Ka kori jar naggen can

    Mai cin jar dawar can

    Ta jar gonar can

    Ta jan mutumin can.

     

    Tabbas! jar sanda da jar nagge da jar dawa da jar gona akwai abubuwan hangowa a ciki na nagarta. Jar sanda dole ta kasance kulki. Jar nagge babu wai ga kasancewarta karsana. Jar dawa kuwa ko a magani mahaÉ—in maganin mazakuta ce.

    Ficen “jan” Launi ga Mu’amular Tsaro da Buwaya

    Gobirawa mayaÆ™a ne gaba da baya, kuma masana ne a kan harkokin tsaro da dabarun yaÆ™i. Saka launin “ja” cikin kirarin “Bawa” wani karatu ne babba. Idan muka yi nazari za mu ga cewa:

    1)    Barkono ja ne, jajir da shi ga shi da tsananin yaji, hatta da tattasai da tarugu da suka zo da baya ba sa ciyuwa idanu ba su yi hawaye da ja ba. Nagartar namiji jan ido ya sa idanu kuka.

    2)    Jini na kowace irin haliita “ja” ne rinjayen launinsa da an ga ya fito a kowane sashe na jikin mai rai razana za ta shiga. Da yaro da babba babu wanda jini ba ya wa barazana. Haka ake son shugaba tsakanin mabiya.

    3)    Wuta, belanta da farshinta da garwashinta duk jajaye ne, kuma jajirtattu. Da mai hankali da maras hankali ba wanda wuta ba ta sa wa hankali ba. Gaskiyar Bahaushe da yake cewa, yaro bai san wuta ba sai ya dafa. Haka kuma ake da karin maganar, wuta ba ta da raggon doki.

    4)    Da belar wuta, da ruÉ“ushinta, da gaushinta duk jajaye ne. Ko a wasan maÆ™era takin “kunkurun tama” Æ™arfen da aka saka a wuta ya yi jajir sai maÆ™eran da suka tambayu. Don haka “ja” a cikin suna nagarta da jarunta yake tabbatarwa.

    5)    A yi duba zuwa ga bindigoginmu da sojojimu ke amfani da su, a kowace bindiga Æ™arshenta daidai wurin da balbalin bala’i ke tartsatsi sukan É—aura É—an Æ™yalle ko tsumma “ja”. A gargajiyance suturar dogarai ‘yan Æ™asa na sarakunanmu “ja” ne. Haka kuma, rawunnan dogarai “ja” ne. Kuben kowane irin makamin Bahaushe za a ga “ja” ne da aka yi da jemammiyar fata “ja”. Kai! hatta da jar dawa É“awonta “ja” ne da shi ake yin sarrafa jan launi a waÆ™oÆ™i.

      Yadda muka ga fasulan jan launi a daÉ—aÉ—É—un adabin baka haka nan adibban mawaÆ™a suka aro su suka sarrafa su a waÆ™oÆ™insu a jigoginsu na yabo ta fuskar jaruntaka da Æ™wazo da Æ™warjini. Ashe dai Gobirawa bisa kan hanya suke idan muka kalli yadda É—aya daga cikin mawaÆ™insu Dr. Ibrahim AbdulÆ™adir Maidangwale NarambaÉ—a ya kambama Æ™warewa da adalci da Æ™wazon AlÆ™ali Abubakar, AlÆ™alin Moriki a faÉ—arsa:

    Jagora: Bilhaƙƙi amali na Jandamo,

    Jagora: Abu hukumul ƙadil madhaa,

    Yara   : In yai magana ta kwakkwahe.

    Gindi  : Ya É—au girma ya san yabo,

                : Mu zo mu ga Alkali Abu.

    Haka za mu ga a cikin waÆ™oÆ™in Amali Sububu yana koÉ—a taurararonsa “Aikau Jikan Tayawa” gawurtaccen manomi da faÉ—ar cewa:

    Jagora: Ku dibi idanun mutum kamar maye.

    Yara  : Jajir ba su da fari.

    Gindi: Ya riƙa aiki da gaskiyar Allah,

              : Bai saba ba da zama,

              : Aikau jikan Tayawa É—an Mamman Kunkelin fashin Æ™asa.

    Wannan ya tabbatar da faÉ—ar Bahaushe na jan ido alamun namiji. Idan abu ya kankama ana saka jan launi wajen yaba shi da É—aukaka shi. Da Shata na yabon Alhaji Garban Bici sai da ya sarrafa jan launi ga yabonsa don ya hanzarta, ya ce:

    Jagora: Kaka ta yi uban Nura,

                 GyaÉ—a ta fara jar fata.

    Gindi  : Haji Garban Bici É—an Shehu.

    A taÆ™aice, mai yabon mazaje jarumai ba ya da makawa ga aron fasahar Gobiawa ta sa wa Sarkin “Jangwarzo”. Bawa ÆŠan’anace a waÆ™arsa da yabon Birgediya Hassan Usman Katsina yana cewa:

    : “Dac can nag ga jan ido.

    A gai da Alhaji Aƙilu Aliyu Birnin Ƙaura Lailai Jega a cikin waƙarsa ta yabon Sojojin Nijeriya, da ta cinye gasa, a wani baiti yana cewa:

    Jar wuta ita ce danja,

    Jar baƙar mutuwa soja.

     HaÆ™iÆ™a sunan Sarki Malam Shekh Umar Bawa Jangwarzo ya zanu domin ya ci sunansa da sifanta shi da aka yi da “jan” launi, yanzu sai mu fayyace abin da ya biyo bayan jan launi mu gani.

    Gwarzo

    A mahangar Ƙamusun G.P. Bargery

    An enegetic, capable worker; a man of pluck and grit.

    A ma’anar “grit” Ƙamusun Ingilishi ya ce:

    Courage and resolve; strength of character.

    A ma’anar “pluck” Ƙamusun Ingilish ya ce:

    Spirited and determiend courege.

    Ke nan za mu fassara ma’anar gwarzo bisa ga waÉ—annan bayanai da cewa:

    Nagartaccen zarumi gawurtacce mai gaba gaƙi ga abin da ya tunkara ko ya tinkaro shi mai zuciya sambai da fargaba ba ya yi mata barazana.

    Kalmar “gwarzo” kalma ce ta nagara bayan an zama nagartacce a hau matsayin jaruntaka a zama jarumi. Idan jarumi ya  Æ™asaita zai hau gadon gwarzantaka a kira shi “Gwarzo” kalmar “Gwarzo” a cikin waÆ™oÆ™in saraua wata babbar fitila ce cikin kalmomin yabo na waÆ™oÆ™in sarauta da yabon gwaraje, a Æ™asar Hausa. Mu dubi gindin waÆ™ar bakandamiyar Dr. Ibrahim NarambaÉ—a da ke cewa:

    Gindi: Gwarzon Shamaki na Malam toron giwa,

              : Baban Dodo ba a tamma da batun banza.

    Wannan ita ce Bakandamiyar Malamin waÆ™ar Æ™asar Hausa kuma da kalmar “gwarzo” ya yi shamaki da ita a gindin waÆ™arsa. MakaÉ—a Dandada ya yi tubali da ita a waÆ™arsa ta:

    Gindi: Gwarzon Galadima ya ci arna,

              : Uban Yari baban Barga na farko.

    Me ya sa Sarkin Gobir Bawa ya keÉ“anta da kalmar “Gwarzo” a cikin sarakunan Æ™asar Hausa? Babban dalili shi ne, saboda kasancewarsa jarumi a fagen yaÆ™i bisa ga yaÆ™e-yaÆ™en da ya gwabza Æ™asa Hausa.

    Ƙasaitar “Jangwarzo” Cikin Gwarajen Sarakunan Sudan

    Ƙasar Hausa wata irin makekiyar Æ™asa ce da ta Æ™unshi al’ummomi masu É—imbin yawa. Ƙasa ce da kowane sarki da Æ™arfin soje yake taÆ™ama da É—iyaucin kare zuriyarsa. Babu zuriya daga cikin zuriyoyin Æ™asar Hausa da ke da raggon suna. Kowace Æ™asa da fitaccen sarkinta take tinÆ™aho da bugun gaba. Ga Æ™unshiyar masarautun da zuriyarsu da kakaninsu.

     

     

    Ƙasa

    Mutanenta

    Birininsu

    Kakaninsu

    Karin Harshensu

    1.      

    Kano

    Kanawa

    Kano

    Bagauda

    Kananci

    2.      

    Katsina

    Katsinawa

    Katsina

    Katsi

    Katsinanci

    3.      

    Kabi

    Kabawa

    B/Kebbi/Argungu

    Kanta

    Kabanci

    4.      

    Zamfara

    Zamfarawa

    Rawayya/Gusau

    Yargoje

    Zamfaranci

    5.      

    Daura

    Daurawa

    Daura

    Daurama/Bayajida

    Dauranci

    6.      

    Zazzau

    Zagezagi

    Zariya

     

    Zazzaganci

    7.      

    Gobir

    Gobirawa

    Sabon Birni

    Jangwarzo

    Gobirarci

    8.      

    Yawuri

    Yawurawa

    Birnin Yauri/Yauri

    Jarbana

    Yawuranci

    9.      

    MaraÉ—i

    MaraÉ—awa

    Maradi

    Tcagarana

    MaraÉ—anci

    10.             

    Damagaran

    Damagarawa

    Zinder

     

    Arabci

    11.             

    Sakkwato

    Sakkwatawa

    Sokoto

    Danfodiyo

    Sakkwatanci

     

    Waɗannan gundumomi da daulolin ƙasar Husa manya da ƙananan sarakunansu fitattu ne kuma shahararru a tarihi amma babu sunan da ya kai na Sarkin gobir Malam Shekh Umar Bawa Jangwarzo amo a cikinsu. Sunan Sarki Bawa da ƙasarsa wani gambu daga cikin gambunan rufe ƙofar fice da ɗaukaka a ƙasar Hausa, da an ce Gobir sunan Sarki Bawa Jangwarzo ke fara faɗowa a zuciyar mai magana da mai sauraronsa.

    Kurya Gangar Mutuwa

    Daulolin nan na Æ™asar Hausa da muka lissafa kowannensu na da É—an taken tarihi na jaruntaka da ake yi masa in an ambace shi. Kowane kirari ko take yana da alaÆ™a da tarihin Æ™asar ko masarautarta ko sarakunanta ko sarkinta ko jama’ar Æ™asarta. Ga É—an abin da nake son in bayyana:

    1.              Sakkwato: Birnin Shehu ta Bello mai da Æ™asari zuma

    2.              Kano: Jalla babbar Hausa, Kano ba gari ba dajin Allah

    3.              Argungu: Na Kanta ba ku da raggo

    4.              Katsina: Dakin Kara

    5.              Yawuri: In ka san Yawuri ka san geshe?

    6.              Gusau: Ta Sambo dandin Hausa

    7.              Zazzau: Zazzau birnin ilmi na Turunku masu kaurin cinya a ba ku ci a ga aiki.

    8.              Daura: Ta Abdu tushen Hausa.

    9.              MaraÉ—i:

    10.         Damagaran:

    11.         Gobir: Uwar faÉ—a ko ta Bawa Uwar faÉ—a

    A taÆ™aice babu Æ™asa daga cikin Æ™asashen nan (11) na Hausa da ake yi wa kirari na “faÉ—a/yaÆ™i" in ba Gobir ba. Ashe Sarkinta ya ci sunansa “Jangwarzo” domin tsakanin sarakuna (10) aka naÉ—a masa rawanin zama gwarzo a fagen yaÆ™i har ya Æ™aura ba a karÉ“e tutar a hannunsa ba. Babu wata Æ™asa ta Sudaniyya da ke tinÆ™aho da da dakaru da Gobir ba ta gwada tsawo da ita ba. Gobirawa ba su taÉ“a kunyata Jangwarzo har bayan ya Æ™aura ba. Don haka mawaÆ™insu ke cewa:

    Jagora: Gobirawa kun sha kunun baƙar zuciya,

    Yara   : Nan gidan duniya babu inda ba a ji ku ba.

    Gobir Gambun Hausa

    Lokacin da Æ™asar Hausa take yau ciwo gobe lafiya a kan yi wa manyan birane da gururuwa ganuwa a sa Æ™yaure/gambu a rufe a naÉ—a sarkin Æ™ofa. Idan an yi haka, ba shiga, ba fita sai da yardar Sarkin Æ™ofa. Irin haka ne Gobir ta kasance wa Æ™asar Hausa. Tsoron Gobirawa da ake yi a fagen daga musamman zamanin Sarkin Gobir Malam Bawa Jangwarzo ya sa Æ™asashe da yawa na jin tsoro kawo hari Æ™asar Hausa. Bayan cin Alkalawa da masu jihadi suka yi 1809, Gobirawa ba su tarwatse ba, domin wasu suka koma Tcibiri, wasu suka bi Yariman Gobir ÆŠanhalima suka sake kafa Sabon Birnin ÆŠanhalima kusa da Kogin Bunsuru (Gobir: 2021:5). A taÆ™aice Gobirawa sun yaÆ™i Kabi a Æ™arni na 18th, Zamfara ta rushe a Æ™arni na 14th C, Katsina 1764. Don haka, da Katsina da Zamfara da Kabi sun yi wa Gobir gambu babu mai ratso su shi kai mata hari, ita kuwa ta yi musu gambu babu wanda zai tunkare ta da yaÆ™i, domin ya san suna tare (‘Yandaki: 2021:11). Bugu da Æ™ari Gobir ta gwabza da Azbin da Adar a Æ™arni na 7th C, a nan ma ta yi wa Æ™asar Hausa gambu ga masu Æ™etaro kashin giwa su ce su shigo Æ™asar Hausa. Gobirawa suka fara kafa dangantaka mai Æ™arfi da Æ™asashen nesa ga Æ™asar Hausa irin su Yemen, Saudi Arabiya, Egypt, Sudan da Daular Borno, a tarihin                   Æ™aurace-Æ™auracensu duk suna da danganta da su, wanda ya Æ™ara wa ganuwar Æ™asar Hausa da Æ™yaurenta Æ™arfi sosai.

     

     

    Ja da Baya ga Rago

    Hausawa na cewa: Ja da baya ga rago ba tsoro ba ne duk cikin shirin yaÆ™i ne. Babu gwarzon duniya da zai bugi Æ™irjin cewa ba a taÉ“a ribantarsa ba. Wurin da gizo ke saÆ™a shi ne, a karaya a gudu a tsere a yi hijira, a ce an tuba da faÉ—a wanda ba ya cikin kundin tarihin Gobirawa. Duk da haka, Gobirawa sun yarda da a share jini a koma wasa, sai dai ba su yarda da faÉ—an da ya fi Æ™arfinka ka mai da shi wasa ba. Domin su a wajensu yaÆ™i shiga sojan Badakkare ne, in til, in Æ™wal rinin mahaukaciya. YaÆ™e-yaÆ™ensu ya ba su damar wasanni tsakaninsu da Zamfarawa, Fulani, Yorubawa, Katsinawa da zumunta da Kabawa. Babu wai, zancen a mazaya a mayar da iri gida ya yi naso a yaÆ™in Dutsen wake a Æ™asar Kiyawa (Ibrahim: 2021:343) da yaÆ™in ÆŠanÆ™asawa zamanin Ummaru Dallaje (1807-1835) Gobir agaji ta bayar da yaÆ™in ci-kaji (1978) zamanin Sarkin Gobir Ibrahim Shawai, agaji Gobir ta kai. Ga al’adar faÉ—a da yaÆ™i da jihadi, yaudara da salon ja da baya a sake shiri ba kasawa ba ne, cikin dabarun fama ne da suke shiri.

    Sakamakon Bincike

    Tunanin wannan bincike shi ne duba zuwa ga jagoran Gobirawa da ya fi kowane sarki daga cikin sarakunan Gobir fice da kere ga suna. Abu na farko da na gano, Sarki Umaru Bawa Jangwarzo martaba uku yake da su da suka zama tsani ga É—aukakarsa. Na farko Basarake ne gaba da baya. Na biyu, Malamin addini ne, ko an Æ™i a faÉ—a don hasada. Na uku jarumi ne, jarumi uban gidan jarumai don haka aka ba shi laÆ™abin JANGWARZO. Irin tsayin dakar da Sarkin Gobir Malam Umar Bawa Jangwarzo ya yi na hanawa magabta ratsa Æ™asarsa, da yi mata gambu da Æ™asashen da ya yaÆ™a, da hana ta miÆ™a wuya da kasancewa Æ™arÆ™ashin kowace irin daula ta kowace irin jinsin mutane Æ™arÆ™ashin kowane irin salo shi ne musabbabin haÉ—in kan Gobirawa da Æ™asaitarsu a farfajiyar Sudaniyya. Sarki Bawa ya tsare wa Gobirawa Æ™asarsu, tarihinsu, addininsu, al’adunsu, da É—iyaucinsu, ya girka wa Gobirawa kishin Æ™asarsu a zukatansu wanda ya hana wa Gobirawa É—aga hamata ga kowace Æ™abila da ke son ta yi musu shigar kutse. Na dai tabbata sunan JANGWARZO ya cancanci Bawa domin ya mayar da ragon suna.

    NaÉ—ewa

    Daga cikin zuriyar Hausawa da ke zaune a Æ™asar Hausa babu zuriyar da ta fi ta Gobirawa haÉ—in kai. Babu wani lungu daga cikin lungunan Æ™asarmu Nijeriya da Gobirawa ba su yi sansani ba. A cikin Afirka ta Yamma sun barbazu sosai da sana’o’i daban-daban. Gobirawa na daga cikin zuriyar Hausawa da suka kiyaye dangin jininsu da sarautunsu da kadadar Æ™asarsu. Tsagar fuskarsu ta daban ce, ba a yin ta ga duk wanda ba ga uba ya gaji Gobarci ba, kuma ba su yarda da aron tsagar fuskar kowa ba. Biyayyarsu ga shugabanci da gabaci ya sa, har gobe ba su daina yi wa ‘ya’yansu laÆ™abi da sunan Sarkin Gobir Malam Bawa Jangwarzo ba. Haka kuma babu basaraken da ya ari sunan “Jangwarzo” har yau. Abin ban sha’awa na taÉ“a tambayar wani bakaniken motoci marsandi a Buzaye mai suna Aliyu ma’anar Lambar SBN (Sabon Birni) ya ce: S. Shehu, B. Bello, N. Nana Asma’u. Allahu akbar! A share jini a koma wasa, lallai sarkin Gobir Shekh Malam Umar Bawa Jangwarzo ya ci sunan SARKI ba Sarkin Æ™aÆ™e ba.

    Manazarta

     Ahmad, S. A. (2021) “Waiwayen Sarautun Mata Na Daular Gobir da   Yadda Za a FarfaÉ—o da Su.” Cikin Maishanu, I. M., Usman, M.T.     da     Gobir, A. Y. (Editoci). Proceeding International Conference on     Transformations in Gobir  Kingdom Past and        Present,Pp.369-377.     Published By Faculty of Arts and Islamic Studies, Usmanu    Danfodiyo          University, Sokoto. Kaduna: Amal           Printing Press.

     

    Aliyu, A. “WaÆ™ar Yabon Sojojin Nijeriya.”

     Ammani, M. (2021) “Gurbin Gaskiya a Bakin MakaÉ—an Gobir: Tarke    Daga           WaÆ™ar AlÆ™ali Abu ta Ibrahim NarambaÉ—a.” Ciikin Maishanu,       I. M., Usman,      M.T. da     Gobir, A. Y.(Editoci). Proceeding International Conference on           Transformations in Gobir Kingdom          Past and Present, Pp.393-405. Published By Faculty of Arts and         Islamic Studies,UsmanuDanfodiyo University, Sokoto. Kaduna:        Amal Printing Press.

     

    Augi, A. R. (1984) “The Gobir Factor in the Social and Political History of      the Rima Basin” (Circa 1650-1808), PhD thesis, Zaria: Ahmadu Bello University Vol.1.

     

    Bargery, G. P. (1993) A Hausa-English Dictionary and English- Hausa           Vocabulary (Second Edition). Zaria: Ahmadu Bello University Press           Limited.

     

    Bunza, A.M. (2009) NarambaÉ—a, Ibrash, Lagos: Surulere.

     

    Bunza, A. M., Sarkin Sudan, I. A., Usman, B. B. (2009) Daular           Sakkwato(Fassarar Sokoto Caliphate na Mury Last). Lagos: Ibrash      Islamic Publication Centre Limited.

     

    Bunza, A. M. (2021) “Ba a Wane Baki Banza (Gurbin Daular Gobir da           Gobirawa a Farfajiyar Sudaniya.” Cikin Maishanu, I. M., Usman,           M.T. da     Gobir, A. Y. (Editoci). Proceeding International       Conference on           Transformations in  Gobir Kingdom Past and   Present, Pp.242-259.           Published By Faculty of Arts and Islamic     Studies, Usmanu Danfodiyo           University, Sokoto. Kaduna: Amal      Printing Press.

     

    Danmode, H. O. (2021) “Re-Enacting the Place and Position of Gobir    Kingdom Beyound the Confines of Nigeria.” Cikin Maishanu, I. M.,    Usman,  M.T. da  Gobir, A. Y.(Editoci). Proceeding International        Conference on Transformations in Gobir Kingdom Past and        Present, P.7-10. Published By Faculty of Arts and Islamic       Studies,Usmanu         Danfodiyo          University, Sokoto. Kaduna: Amal         Printing Press.

     

    Furniss, G. (1996) Poetry Prose and Popular Culture in Hausa. EU:           Edinburgh.

    Gobir, A. Y. (2016). “Gobir Wani Jigo a Ƙasar Hausa: Waiwayen Tarihi          da Diddigin Masarautun Gobir.” A cikin Malumfashi, I. A., Yakasai,          S. A., da Sarkin Sudan, I. A. (editoci). The Hausa People, Language        and    History: Past Present and Future. Kaduna: Garkuwa Publishers.

    Hisket, M. (1975) A History of Hausa Islamic Verse. London: School of           Oriental and African Studies, (SOAS).

    Ibrahim, A. (2021) “Hoton YaÆ™e-yaÆ™en Gobirawa da Katsinawa Cikin  Karin Maganar “A Mazaya a Mai da Iri Gida.” Cikin    Maishanu, I.       M.,    Usman, M.T. da      Gobir, A. Y. (Editoci).          Proceeding International Conference on Transformations in Gobir Kingdom Past and Present, Pp.334- 347. Published By Faculty of Arts and    Islamic Studies, Usmanu Danfodiyo University, Sokoto. Kaduna:    Amal Printing Press.

     

    Last, M. (1967) “Sokoto Caliphate.” PhD thesis, Ibadan: University of  Ibadan.

     

    Mamman, J. S. (2014) “A Literary Analysis of the Themes and Imagery in           Amali Sububu’s Songs.” M.A Thesis, Sokoto: Department of         Modern European Languages and Linguistics, Usmanu Danfodiyo   University.

     

    Sani, A., Gobir, A. Y. (2021) Wasanni a Ƙasar Hausa. Kaduna: Amal         Printing Press.

     

     Sarkin Sudan, I. A. (2021) “Gobarci: Tsagar Gobirawa a Faifan Nazari.”           Cikin Maishanu, I. M.,        Usman, M.T. da          Gobir, A. Y. (Editoci).           Proceeding International Conference on   Transformatuions in Gobir    Kingdom           Past and Present, Pp.384- 392. Published By Faculty of   Arts and    Islamic Studies, Usmanu Danfodiyo University,      Sokoto.Kaduna:          Amal Printing Press.

     

    Yandaki, A. I., Gusau, S. S., & Yandaki, U. A. (2021) “Gobir External     Relations in the 18th Century.” Cikin Maishanu, I. M., Usman, M.T.    da Gobir, A. Y. (Editoci). Proceeding International Conference on     Transformatuions in Gobir Kingdom Past and Present, Pp.11- 24.     Published By Faculty of Arts and Islamic Studies, Usmanu        Danfodiyo          University, Sokoto.Kaduna:         Amal Printing Press.

    No comments:

    Post a Comment

    ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.

    HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.