Idan Kika Kirata A Waya Kukai Fada To A Bakin Aurenki, Sai Ta Kira Da Private Number

    TAMBAYA (20)

    Assalam (Tambayace) Shigen wanda ya ce in ta fita ta kofar nan abakin auranta

    Toshima kusan hakanne Tace seta kirata sunyi fada taci mata mutunchi snn ta fada mata fa tasan meke tsakanin su Shine shikuma ya ce inta kirata tai mata hakan abakin auran ta Ita kuma seta kira da private number batai mgn ba tai tsaki kawai ta kashe

    AMSA

    Waalaikumussalam. Waalaikumussalam. Wabarakatuhum.

    Sakin da aka saka sharadin anyishi silar fita ta kofa shi ake kira "Talaq al-bab" a shari'a wanda an samu sabanin malamai sosai akan tabbatuwarsa

    Wasu malaman sukace sakin da miji yayi akan sharadin matar ta fita ta window bai tabbata ba saboda ai sharadin shine sai ta bi ta kofa

    Wasu kuma malaman sukace idan ta fita ta window dukda sharadin mijin shine ta kofa to kawai ta saku saboda muhallish shahid din shine fita daga gidan baki daya

    Wasu malaman sukace saki daya ne wasu kuma sunce uku ne wasu kuma sukace kamata yayi a tambayi mijin me yake nufi da a bakin aurenta ?

    To kamar hakane idan ya zamana ta kira waccan ta private number tunda ba kiranta tayi direct ba

    Sai aji ta bakinsa shin saki yake nufi ko kuma gargadi yake mata kada ta kira matar don ya tsoratata

    Wannan shine ra'ayin da muka tafi akai, in sha Allah

    Domin karin bayani sai a duba Alwajiz Fi fiqhis Sunnah a cikin babin saki (Talaq)

    A karshe ina son na ja hankalin matan aure su daina wasa da al'amarin saki. To in banda ma biyewa shaidan da son zuciya menene alfanun kiranta ta private. Kada ku mantafa Aljannar matar aure tana duga-dugan mijinta (ta hanyar yi masa biyayya) Kamar yanda Annabi SAW yabawa Ummu Adiyya RA amsa lokacinda ta tambayeshi maza suna zuwa makabarta an hani mata da zuwa, maza suna yin yaqi mata basayi, ta yaya mata zasu kamo maza a daraja sai ya ce (SAW) biyayya ga mijinta. Yayinda kuketa sabawa umarnin miji wasu suna can mijin suje nema ruwa a jallo basu samu ba. Allah ya shiryemu ya bamu ikon gyarawa

    Wallahu ta'ala a'alam

    Amsawa:

    Usman D. Mato (Usmannoor_As-salafy)

    https://chat.whatsapp.com/GcU1I5wjOB18K4PA6eURQQ

    Question and Answers in Islam

    No comments:

    Post a Comment

    ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.

    HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.